< Titus 2 >
1 Dole ka koyar da abin da yake bisa sahihiyar koyarwa.
But do thou speak the things which become sound doctrine:
2 Ka koya wa tsofaffin maza su kasance masu sauƙinkai, waɗanda suka cancanci girmamawa, masu kamunkai, sahihai wajen bangaskiya, da ƙauna da kuma jimiri.
that aged men be sober, grave, temperate, sound in the faith, in love, in patience:
3 Haka ma, ka koya wa tsofaffin mata su zama masu bangirma cikin rayuwarsu, ba masu ɓata suna ko masu jarrabar shan giya ba, sai dai su zama masu koyar da abin da yake nagari.
the aged women likewise in behaviour as becometh saints, not false accusers, not given to much wine, teachers of that which is good;
4 Sa’an nan za su iya su koya wa mata masu ƙuruciya su ƙaunaci mazansu da’ya’yansu,
that they may instruct the young women to be temperate, to love their husbands, to love their children, to be prudent,
5 su kasance da kamunkai da kuma tsarki, masu aiki a gida, masu kirki da kuma masu biyayya ga mazansu, don kada wani yă rena maganar Allah.
chaste, keepers at home, good, submissive to their husbands, that the word of God may not be evil spoken of.
6 Haka kuma, ka ƙarfafa samari su zama masu kamunkai.
Exhort the young men in like manner to be temperate:
7 Cikin kowane abu ka zama musu misali mai kyau ta wurin aikata abin da yake nagari. A cikin koyarwarka ka nuna mutunci da ƙwazo
in all things shewing thyself a pattern of good works, with uncorruptness in teaching, gravity, sound doctrine that cannot be condemned;
8 da kuma sahihanci cikin maganar da ba za a iya kushewa ba, domin masu gāba da kai su ji kunya, su kuma rasa wani mugun abin da za su faɗa game da mu.
that he who opposeth it may be ashamed, having no evil to say of you.
9 Ka koya wa bayi su yi wa iyayengijinsu biyayya cikin kowane abu, su yi ƙoƙari su gamshe su, kada su mayar musu da magana,
Exhort servants to submit to their masters, to be obsequious in all things,
10 kada kuma su yi musu sata, sai dai su nuna za a iya amince da su sosai, don ta kowace hanya su sa koyarwa game da Allah Mai Cetonmu ta zama abin ɗaukan hankali.
not answering frowardly, not purloining, but shewing all good fidelity; that they may adorn the doctrine of God our Saviour in all things.
11 Gama alherin Allah mai kawo ceto ya bayyana ga dukan mutane.
For the grace of God, that bringeth salvation, hath appeared to all men;
12 Yana koya mana mu ce, “A’a” ga rashin tsoron Allah da kuma sha’awace-sha’awacen duniya, mu kuma yi rayuwa ta kamunkai, ta adalci da kuma ta tsoron Allah a cikin wannan zamani, (aiōn )
teaching us that denying ungodliness, and worldly desires, we should live soberly, and righteously, and piously in this present world; (aiōn )
13 yayinda muke sauraron begenmu mai albarka bayyanuwar ɗaukakar Allahnmu mai girma da kuma Mai Cetonmu, Yesu Kiristi,
looking for the blessed hope, and glorious appearance of the great God, and our Saviour, Jesus Christ:
14 wanda ya ba da kansa dominmu don yă fanshe mu daga dukan mugunta yă kuma tsarkake wa kansa mutanen da suke nasa, waɗanda suke marmarin yin abin da yake nagari.
who gave Himself for us, that He might redeem us from all iniquity, and purify to Himself a peculiar people, zealous of good works.
15 Waɗannan kam, su ne abubuwan da ya kamata ka koyar, ka ƙarfafa ka kuma tsawata da dukan iko. Kada ka yarda wani yă rena ka.
These things speak, and exhort; and reprove offenders with all authority: that none may despise thee.