< Waƙar Waƙoƙi 4 >

1 Ke kyakkyawa ce, ƙaunatacciyata! Kai, ke kyakkyawa ce! Idanunki sun yi kamar na kurciya a cikin lulluɓinki. Gashinki ya yi kamar garken awaki da suke gangarawa daga Dutsen Gileyad.
Kayisibuhle bakho, sithandwa sami! Awu, ayisibuhle, bakithi! Amehlo akho embeswe liveli, angamajuba. Inwele zakho zinjengomhlambi wembuzi zisehla entabeni iGiliyadi.
2 Haƙoranki sun yi kamar garken tumakin da ba a daɗe da yin musu sausaya ba, da suke haurawa daga inda aka yi musu wanka. Kowanne yana tare da ɗan’uwansa; babu waninsu da yake shi kaɗai.
Amazinyo akho anjengomhlambi wezimvu zisanda kugundwa, zivela geziswa yileyo ihamba laleyo efanana layo; kayikho ethe qekele yodwa.
3 Leɓunanki kamar zaren jan garura bakinki yana da kyau. Kumatunki sun yi kamar rumman da aka tsaga biyu a cikin lulluɓinki.
Izindebe zakho zinjengozwezwe olubomvu; muhle umlomo wakho. Izihlathi zakho ezembeswe liveli lakho ezinjengephomegranathi elidatshulwe phakathi.
4 Wuyanki ya yi kamar hasumiyar Dawuda, da aka gina da daraja; a kansa an rataye garkuwoyi dubu, dukansu garkuwoyin jarumawa ne.
Intamo yakho injengomphotshongo wokulinda kaDavida, owakhiwa waba muhle kakhulu; kulengiswe kuwo amahawu ayinkulungwane, wonke angamahawu amaqhawe.
5 Nonanki biyu sun yi kamar bareyi biyu, kamar tagwayen barewa da suke kiwo a cikin furen bi-rana.
Amabele akho omabili anjengamazinyane amabili, njengamaphahla amazinyane empala adla utshani phakathi kwezimbali.
6 Sai gari ya waye inuwa kuma ta watse, zan je dutsen mur da kuma tudun turare.
Nxa kusesemadabukakusa izithunzi zingakabaleki emuntwini, ngizakuya entabeni yemure laseqaqeni lwamakha amnandi.
7 Duk, ke kyakkyawa ce, ƙaunatacciyata; babu wani lahani a cikinki.
Umuhle kakhulukazi, ntokazi yami; kakulanto engenhle kuwe.
8 Ki tare da ni daga Lebanon, amaryata, zo tare da ni daga Lebanon. Ki gangara daga ƙwanƙolin Amana, daga ƙwanƙolin Senir, ƙwanƙolin Hermon, daga ramin zaki da kuma dutsen da damisoshi suke zama.
Woza, mlobokazi wami, sisuke eLebhanoni, woza sisuke eLebhanoni. Yehla emaweni ase-Amana, wehle esiqongweni saseSeniri, isiqongo seHemoni, ezimbalwini zezingonyama lezintabeni okuhlala ingwe kuzo.
9 Kin saci zuciyata,’yar’uwata, amaryata; kin saci zuciyata da hararar idanunki, da dutse mai daraja guda na abin wuyanki.
Uyithumbile inhliziyo yami, dadewethu, mlobokazi wami; uyithumbile inhliziyo yami ngokungithi jeqe ngamehlo akho, langengqongqo elilodwa lobuhlalu bakho.
10 Ƙaunarki abar farin ciki ne,’yar’uwata, amaryata! Ƙaunarki ta fi ruwan inabi gamsuwa, ƙanshin turarenki kuma ya fi duk wani kayan yaji!
Luthokozisa kanganani uthando lwakho, dadewethu, mlobokazi wami! Lumnandi kakhulu kulewayini, lephunga lamakha akho kulawo wonke amafutha!
11 Leɓunanki suna zub da zaƙi kamar kakin zuma, amaryata; madara da zuma suna a ƙarƙashin harshenki. Ƙanshin rigunanki ya yi kamar na Lebanon.
Izindebe zakho ziconsa ubumnandi njengoluju, mlobokazi wami; uchago loluju kungaphansi kolimi lwakho. Iphunga lezivunulo zakho linjengeleLebhanoni.
12 Ke lambu ne da aka kulle,’yar’uwata, amaryata; ke maɓulɓula ce da aka kewaye, maɓulɓular da aka rufe.
Uyisivande esibiyelweyo, dadewethu, mlobokazi wami; ungumthombo obiyelweyo, lesiphethu esihuqelweyo sagcikwa.
13 Shuke-shukenki gonar rumman ne da’ya’yan itace masu kyau na lalle da nardi,
Izilimo zakho ziyisivande samaphomegranathi alezithelo ezinhle zilehena lenadi,
14 nardi, da asfaran, kalamus, da kirfa, da kowane irin itacen turare, da mur da aloyes da kuma dukan kayan yaji masu kyau.
inadi lesafuroni, ikhalamu lesinamoni, lemihlobo yonke yezihlahla zempepha, imure lenhlaba lazozonke iziyoliso zekhethelo.
15 Ke lambun maɓulɓula ne, rijiya mai ruwan da yake gudu yana gangarawa daga Lebanon.
Uyisiphethu sesivandeni, umthombo ogeleza amanzi ugeleza usehla eLebhanoni.
16 Farka, iskar arewa, ki kuma zo, iskar kudu! Hura a kan lambuna, don ƙanshinsa yă bazu har waje. Bari ƙaunataccena yă zo cikin lambunsa yă ɗanɗana’ya’yan itacensa mafi kyau.
Vuka moya wenyakatho, woza moya weningizimu! Phephetha esivandeni sami, ukuze amakha aso agcwale indawo yonke. Akuthi isithandwa sami size esivandeni saso sikholise izithelo zaso zekhethelo.

< Waƙar Waƙoƙi 4 >