< Waƙar Waƙoƙi 3 >

1 Dare farai a kan gadona na nemi wanda zuciyata take ƙauna; na neme shi amma ban same shi ba.
Mounu: Jan khat khun chunga sa-mang kajal laijin, ka goldeipa ka lhangai lheh-e. Kalhangai lheh jeng in, hinlah ama ahung poi.
2 Zan tashi yanzu in zagaya gari, in ratsa titunansa da dandalinsa; zan nemi wanda zuciyata take ƙauna. Saboda haka na neme shi, amma ban same shi ba.
Hijeh chun, “Keima kithoudoh-ing katin khopi tolsungah vahle in, lamlen-lamkah ningkoi jouse ah ka goldeipa gahol le inge,” tin ka kigel tai. Hiti chun ka gahol le in, hinlah ka gamu joupoi.
3 Masu tsaro suka gamu da ni yayinda suke kai kawo a cikin birni, sai na ce, “Kun ga mini wanda zuciyata take ƙauna?”
Kholai vengtup jan khongah hon lamkah-a eina khamtang uvin, chuin keiman amaho jah-a, “Ka goldeipa chu namu khah uvem?” tin kadong’e.
4 Rabuwata da su ke nan sai na sami wanda zuciyata take ƙauna. Na riƙe shi, ban yarda yă tafi ba sai da na kawo shi gidan mahaifiyata, zuwa ɗakin wadda ta yi cikina.
Amaho ka dalhah jouchet’na ka goldeipa kamu-mu chun, ka nailut in ka tuhchah jeng tan, chuin kapenna indan, kanu insung ah ka puilut tai.
5 ’Yan matan Urushalima, ku yi mini alkawari da bareyi da ƙishimai na jeji. Ba za ku tā da ko ku farka ƙauna ba sai haka ya zama lalle.
Vo Jerusalem chanute, loujaova sapeng le sakhi min pan’a katem nahiuve; achama ahung kipatdoh ngal lou leh kideina hi nanghon tildoh tho ding le suhkhah-tho din got dauvin.
6 Wane ne wannan mai zuwa daga hamada kamar tunnuƙewar hayaƙi, cike da ƙanshin turaren mur da lubban da aka yi da kayan yajin’yan kasuwa?
Zailom: Ipi hitantem hiche gamthip lama kon’a meikhu lom banga kijel doh letlut pi khu? Ipi hitan tem Myrrh gim namtwi chule sumkol veiho gimnamtwi kilhut nam bang jeng hi?
7 Duba! Abin ɗaukar Solomon ne, jarumawa sittin suke rakiya, zaɓaɓɓun sojojin Isra’ila,
Veuvin, hiche khu Solomon khunjon ahi in, avengtup din Israel sunga gamngah-galsat son-um pen pasal thahat somgup in ahin jui uve.
8 dukansu suna saye da takobi dukansu ƙwararru ne a yaƙi, kowanne da takobinsa a rataye a gefensa, a shirye don abubuwan bantsoro na dare.
Amaho khu chemjam peithem cheh, galsat them cheh ahiuve. Chemjam a kiko sohkei uvin, janteng koiyin lengpa hin bulu jongleh avengdoh ding sadema kimansa ahiuve.
9 Sarki Solomon ya yi wa kansa abin ɗauka; ya yi shi da katako daga Lebanon.
Leng Solomon loupitah-a akijonna khunjon hi Lebanon gam'a thing phapen’a kisem ahi.
10 An yi sandunansa da azurfa, aka yi ƙasarsa da zinariya. An lulluɓe wurin zaman da zanen shunayya,’yan matan Urushalima sun yi mata irin yayen da ake yi na ƙauna.
Akhun jon akhom-ajol chengse chu dangka jeng in a kisem in, achung khu khu sana songmantam in akitom in, apondal-ho chu pon san dup val lheng ahi. Hichu Jerusalem chanu ten ngailutna jouse puma ajep-hoisel’u khunjon ahi.
11 Fito, ku’yan matan Sihiyona, ku ga Sarki Solomon yana saye da rawani, rawanin da mahaifiyarsa ta naɗa masa, a ranar aurensa, a ranar da zuciyarsa ta yi farin ciki.
Mounu: Vo Jerusalem chanute, hung uvin lang Leng Solomon hi hung ve tem’un. Aman akipa thanop napen, ajinei nia anun lallukhuh apeh chu akikhuh-in ahi.

< Waƙar Waƙoƙi 3 >