< Rut 4 >

1 Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
Boas gick upp i porten, och satte sig der. Och si, när arfvingen gick derfram, talade Boas till honom, och sade: Kom, och sätt dig här, ehuru ditt namn är. Och han kom, och satte sig.
2 Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
Och han tog tio män af de äldsta i staden, och sade: Sätter eder här. Och de satte sig.
3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
Då sade han till arfvingan: Naemi, som ifrå de Moabiters land igenkommen är, bjuder ett stycke åker fält, som hörde vår broder EliMelech till.
4 Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
Derföre tänkte jag, att jag skulle det kungöra dig, och säga: Vill du komma det i ditt arf, så köp det inför borgarena, och inför de äldsta af mitt folk. Vill du ock icke kommat i ditt arf, så säg mig det, att jag må veta det; ty här är ingen arfvinge till, annar än du, och jag näst dig. Han sade: Jag vill komman i mitt arf.
5 Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
Boas sade: När du köper åkren af Naemis hand, så måste du ock taga Ruth, den Moabitiskon, dens dödas hustru, att du må uppväcka dem döda namn till hans arfvedel.
6 Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
Då sade han: Jag kan icke blifva vid arfvet, att jag tilläfventyrs icke förderfvar min arfvedel. Lös du hvad jag lösa skulle, ty jag kan icke lösan.
7 (To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
Och det var en gammal sedvänja i Israel, när en någon ting icke ärfva eller köpa ville, till att all ting skulle fast blifva, så drog han sin sko utaf, ock fick dem andra; det var då till ett vittnesbörd i Israel.
8 Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
Och arfvingen sade till Boas: Köp du det; och drog sin sko af.
9 Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
Och Boas sade till de äldsta, och till allt folket: I ären i denna dag vittne, att jag hafver köpt allt det EliMelech, och allt det Chilion och Mahlon tillhörde, utaf Naemis hand.
10 Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
Dertill tager jag ock Ruth, den Moabitiskon, Mahlons hustru, mig till hustru, att jag må uppväcka dem döda namn i hans arfvedel, och hans namn icke skall utrotadt varda ibland hans bröder, och utu hans rums portar; dess ären I vittne i denna dag.
11 Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
Och allt folket, som i portenom var, samt med de äldsta, sade: Vi äre vittne; Herren göre den qvinnona, som kommer i ditt hus, såsom Rachel och Lea, hvilka båda hafva uppbyggt Israels hus; och blif ärlig hållen i Ephrata, och var namnkunnig i BethLehem.
12 Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
Och ditt hus vare såsom Perez hus, hvilken Thamar födde Juda, utaf den säd, som Herren dig gifvandes varder af denna qvinnone.
13 Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
Så tog Boas Ruth, att hon vardt hans hustru; och när han låg när henne, gaf Herren henne, att hon vardt hafvandes, och födde en son.
14 Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
Då sade qvinnorna till Naemi: Lofvad vare Herren, som hafver låtit dig icke fattas arfvinga i denna tiden, att hans namn må blifva i Israel.
15 Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
Han varder dig kommandes till lif igen, och försörjandes dig i dinom ålder; ty din sonahustru, som dig älskat hafver, hafver födt den dig bättre är än sju söner.
16 Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
Och Naemi tog barnet, och lade det i sitt sköt, och vardt dess amma.
17 Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
Och hennes grannhustrur gåfvo honom ett namn, och sade: Naemi är födt ett barn; och de kallade honom Obed; han är Isai fader, som är Davids fader.
18 Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
Detta är Perez börd: Perez födde Hezron;
19 Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
Hezron födde Ram; Ram födde Amminadab;
20 Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Amminadab födde Nahesson; Nahesson födde Salmon;
21 Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
Salmon födde Boas; Boas födde Obed;
22 Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.
Obed födde Isai; Isai födde David.

< Rut 4 >