< Rut 4 >
1 Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
Agora Boaz subiu até o portão e sentou-se lá embaixo. Eis que o parente próximo de quem Boaz falou passou por aqui. Boaz disse-lhe: “Venha aqui, amigo, e sente-se”. Ele veio até aqui e sentou-se.
2 Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
Boaz levou dez homens dos anciãos da cidade, e disse: “Sente-se aqui”, e eles se sentaram.
3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
Ele disse ao parente próximo: “Naomi, que voltou do país de Moab, está vendendo a parcela de terra, que era de nosso irmão Elimelech.
4 Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
Achei que deveria dizer-lhes, dizendo: “Comprem-no diante daqueles que se sentam aqui, e diante dos anciãos do meu povo”. Se você vai resgatá-la, resgate-a; mas se você não vai resgatá-la, então me diga, que eu posso saber. Pois não há ninguém que o resgate além de vocês; e eu estou atrás de vocês”. Ele disse: “Eu vou redimi-lo”.
5 Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
Então Boaz disse: “No dia em que você comprar o campo da mão de Naomi, você deve comprá-lo também de Ruth, a moabita, a esposa do falecido, para levantar o nome do falecido em sua herança”.
6 Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
O parente próximo disse: “Não posso redimi-lo por mim mesmo, para não pôr em perigo minha própria herança. Tome meu direito de redenção para si mesmo; pois não posso redimi-lo”.
7 (To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
Agora, este era o costume no passado em Israel no que diz respeito à redenção e à troca, para confirmar tudo: um homem tirou sua sandália e a deu ao seu vizinho; e esta era a forma de formalizar as transações em Israel.
8 Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
Então o parente próximo disse a Boaz: “Compre-a para você”, depois ele tirou sua sandália.
9 Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
Boaz disse aos anciãos e a todo o povo: “Vocês são testemunhas hoje, que comprei tudo o que era de Elimelech, e tudo o que era de Chilion e Mahlon, da mão de Naomi.
10 Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
Além disso, Ruth, a moabita, esposa de Mahlon, eu comprei para ser minha esposa, para levantar o nome dos mortos em sua herança, para que o nome dos mortos não seja cortado de entre seus irmãos e do portão de seu lugar. Vocês são testemunhas hoje”.
11 Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
Todas as pessoas que estavam no portão, e os anciãos, disseram: “Somos testemunhas”. Que Javé faça a mulher que entrou em sua casa como Raquel e como Léia, que construíram a casa de Israel; e o trate dignamente em Efrata, e seja famoso em Belém.
12 Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
Que sua casa seja como a casa de Perez, que Tamar deu a Judá, da descendência que Iavé lhe dará por esta jovem mulher”.
13 Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
Então Boaz levou Ruth e ela se tornou sua esposa; e ele foi até ela, e Yahweh permitiu que ela concebesse, e ela deu à luz um filho.
14 Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
As mulheres disseram a Noemi: “Bendito seja Javé, que não te deixou hoje sem um parente próximo”. Que seu nome seja famoso em Israel”.
15 Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
Ele será para você um restaurador da vida e o sustentará em sua velhice; pois sua nora, que o ama, que é melhor para você do que sete filhos, deu à luz a ele”.
16 Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
Noemi tomou a criança, colocou-o em seu seio e tornou-se enfermeira para ele.
17 Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
As mulheres, suas vizinhas, deram-lhe um nome, dizendo: “Nasceu um filho para Noemi”. Deram-lhe o nome de Obed. Ele é o pai de Jesse, o pai de David.
18 Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
Now esta é a história das gerações de Perez: Perez tornou-se o pai de Hezron,
19 Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
e Hezron tornou-se o pai de Ram, e Ram tornou-se o pai de Amminadab,
20 Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
e Amminadab tornou-se o pai de Nahshon, e Nahshon tornou-se o pai de Salmon,
21 Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
e Salmon tornou-se o pai de Boaz, e Boaz tornou-se o pai de Obed,
22 Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.
e Obed tornou-se o pai de Jesse, e Jesse tornou-se o pai de David.