< Rut 4 >

1 Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
Men Boas var gått op til byporten og hadde satt sig der. Da kom løseren som Boas hadde talt om, nettop forbi, og Boas sa: Kom hit og sett dig her, min venn! Og han kom og satte sig.
2 Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
Så kalte han til sig ti menn av byens eldste og sa: Sett eder her! Og de satte sig.
3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
Derefter sa han til løseren: Den aker som tilhørte vår bror Elimelek, har No'omi solgt, hun som er kommet tilbake fra Moabs land.
4 Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
Og jeg tenkte jeg vilde la dette komme til din kunnskap og si: Kjøp den i overvær av dem som sitter her, og av mitt folks eldste! Vil du innløse den, sa gjør det; men hvis ikke, så si mig det, sa jeg kan vite det! For det er ingen til å innløse den uten du og efter dig jeg selv. Han svarte: Jeg vil innløse den.
5 Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
Da sa Boas: Når du kjøper akeren av No'omi, kjøper du den også av moabittinnen Rut, den avdødes hustru, for å opreise den avdødes navn på hans arvelodd.
6 Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
Løseren svarte: Jeg kan ikke innløse den for mig, for da vilde jeg ødelegge min egen arvelodd; innløs du for dig det jeg skulde løse, for jeg kan ikke innløse det.
7 (To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
I gamle dager var det skikk i Israel ved innløsning og bytte at den ene part til stadfestelse av saken drog sin sko av og gav den til den andre; dette gjaldt som bekreftelse i Israel.
8 Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
Derfor sa løseren til Boas: Kjøp du det! Og med det samme drog han sin sko av.
9 Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
Da sa Boas til de eldste og alt folket: I er idag vidner på at jeg har kjøpt av No'omi alt det som tilhørte Elimelek, og alt som tilhørte Kiljon og Mahlon.
10 Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
Også moabittinnen Rut, Mahlons enke, har jeg vunnet mig til hustru for å opreise den avdødes navn på hans arvelodd, så den avdødes navn ikke skal bli utryddet blandt hans brødre og i hans hjemsteds port; det er I vidner på idag.
11 Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
Og alt folket som var i porten, og de eldste sa: Ja, det er vi vidner på. Herren la den kvinne som nu drar inn i ditt hus, bli som Rakel og Lea, de to som bygget Israels hus, og gid du må bli en mektig mann i Efrata og få en navnkundig sønn i Betlehem!
12 Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
Ditt hus bli som Peres' hus - han som Tamar fødte Juda - ved de efterkommere som Herren vil gi dig med denne unge kvinne!
13 Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
Så tok Boas Rut hjem til sig, og hun blev hans hustru, og han gikk inn til henne; og Herren gav henne livsfrukt, og hun fødte en sønn.
14 Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
Da sa kvinnene til No'omi: Lovet være Herren, som ikke lot dig fattes en løser idag, og han bli navnkundig i Israel!
15 Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
Han skal bli din sjels trøster og din alderdoms forsørger; for din sønnekone, som har dig kjær, har født ham, hun som er mere for dig enn syv sønner.
16 Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
Og No'omi tok barnet og la ham i sitt fang, og hun blev hans fostermor.
17 Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
Og grannekonene gav ham navn og sa: No'omi har fått en sønn! De kalte ham Obed; han blev far til Isai, Davids far.
18 Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
Dette er Peres' efterkommere: Peres fikk sønnen Hesron,
19 Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
og Hesron fikk sønnen Ram, og Ram fikk sønnen Amminadab,
20 Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
og Amminadab fikk sønnen Nahson, og Nahson fikk sønnen Salma,
21 Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
og Salmon fikk sønnen Boas, og Boas fikk sønnen Obed,
22 Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.
og Obed fikk sønnen Isai, og Isai fikk sønnen David.

< Rut 4 >