< Rut 4 >

1 Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
Then Boaz went up to the gate, and sat down there: and behold, the kinsman of whom Boaz spoke came by; to whom he said, Ho, such a one! turn aside, sit down here. And he turned aside, and sat down.
2 Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
And he took ten men of the elders of the city, and said, Sit ye down here. And they sat down.
3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
And he said to the kinsman, Naomi, that has come again out of the country of Moab, selleth a parcel of land, which [was] our brother Elimelech's:
4 Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
And I thought to advertise thee, saying, Buy [it] before the inhabitants, and before the elders of my people. If thou wilt redeem [it], redeem [it]: but if thou wilt not redeem [it], [then] tell me, that I may know: for [there is] none to redeem [it] besides thee; and I [am] after thee. And he said, I will redeem [it].
5 Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
Then said Boaz, What day thou buyest the field of the hand of Naomi, thou must buy [it] also of Ruth the Moabitess, the wife of the dead, to raise up the name of the dead upon his inheritance.
6 Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
And the kinsman said, I cannot redeem [it] for myself, lest I mar my own inheritance: redeem thou my right to thyself; for I cannot redeem [it].
7 (To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
Now this [was the manner] in former time in Israel concerning redeeming and concerning changing, for confirming all things; a man plucked off his shoe, and gave [it] to his neighbor: and this [was] a testimony in Israel.
8 Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
Therefore the kinsman said to Boaz, Buy [it] for thyself. So he drew off his shoe.
9 Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
And Boaz said to the elders, and [to] all the people, Ye [are] witnesses this day, that I have bought all that [was] Elimelech's, and all that [was] Chilion's and Mahlon's, of the hand of Naomi.
10 Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
Moreover, Ruth the Moabitess, the wife of Mahlon, have I purchased to be my wife, to raise up the name of the dead upon his inheritance, that the name of the dead be not cut off from among his brethren, and from the gate of his place: ye [are] witnesses this day.
11 Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
And all the people that [were] in the gate, and the elders said, [We are] witnesses. The LORD make the woman that hath come into thy house like Rachel and like Leah, which two did build the house of Israel: and do thou worthily in Ephratah, and be famous in Beth-lehem:
12 Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
And let thy house be like the house of Pharez, whom Tamar bore to Judah, of the seed which the LORD shall give thee of this young woman.
13 Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
So Boaz took Ruth, and she was his wife: and when he went in to her, the LORD gave her conception, and she bore a son.
14 Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
And the women said to Naomi, Blessed [be] the LORD, who hath not left thee this day without a kinsman, that his name may be famous in Israel.
15 Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
And he shall be to thee a restorer of [thy] life, and a nourisher of thy old age: for thy daughter-in-law, who loveth thee, who is better to thee than seven sons, hath borne him.
16 Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
And Naomi took the child, and laid it in her bosom, and became its nurse.
17 Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
And the women, her neighbors, gave it a name, saying, There is a son born to Naomi; and they called his name Obed: he [is] the father of Jesse, the father of David.
18 Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
Now these [are] the generations of Pharez: Pharez begat Hezron,
19 Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
And Hezron begat Ram, and Ram begat Amminadab,
20 Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
And Amminadab begat Nahshon, and Nahshon begat Salmon,
21 Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
And Salmon begat Boaz, and Boaz begat Obed,
22 Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.
And Obed begat Jesse, and Jesse begat David.

< Rut 4 >