< Rut 4 >

1 Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
But Bo'az went up to the gate, and sat down there; and, behold, the kinsman of whom Bo'az had spoken came passing by; and he said unto him, Turn aside hither, sit down here, such a one. And he turned aside, and sat down.
2 Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
And he took ten men of the elders of the city, and said, Sit ye down here. And they sat down.
3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
And he said unto the kinsman, Na'omi, that is returned out of the field of Moab, hath to sell a parcel of land, which was our brother Elimelech's.
4 Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
And I thought to inform thee of it, saying, Buy it before those sitting here, and before the elders of my people. If thou wilt redeem it, redeem it; but if thou wilt not redeem it, then tell me, that I may know; for there is none beside thee to redeem it, and I am after thee. And he said, I will redeem it.
5 Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
Then said Bo'az, On the day that thou buyest the field out of the hand of Na'omi, thou buyest it also from Ruth the Moabitess, the wife of the dead, to raise up the name of the dead upon his inheritance.
6 Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
And the kinsman said, I am not able to redeem it for myself, lest I injure my own inheritance: redeem thou what I should redeem for thyself; for I am not able to redeem it.
7 (To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
Now this was formerly the custom in Israel at a redeeming and at an exchanging, to confirm any thing, that a man pulled off his shoe, and gave it to the other; and this was the manner of testimony in Israel.
8 Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
Thereupon said the kinsman unto Bo'az, Buy it for thee. And he pulled off his shoe.
9 Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
And Bo'az said unto the elders, and unto all the people, Ye are witnesses this day, that I have bought all that belonged to Elimelech, and all that belonged to Kilyon and Machlon, out of the hand of Na'omi.
10 Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
And also Ruth the Moabitess, the wife of Machlon, have I obtained for myself as my wife, to raise up the name of the dead upon his inheritance, that the name of the dead may not be cut off from among his brethren, and from the gate of his place: ye are witnesses this day.
11 Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
And all the people that were in the gate, and the elders, said, [We are] witnesses. The Lord grant that the woman that is coming into thy house be like Rachel and like Leah, who did both build up the house of Israel: and acquire thou wealth in Ephrathah, and let thy name become famous in Beth-lechem;
12 Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
And may thy house be like the house of Perez, whom Thamar bore unto Judah, through the seed which the Lord will give thee of this young woman.
13 Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
And Bo'az took Ruth, and she became his wife, and he went in unto her: and the Lord gave her conception, and she bore a son.
14 Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
And the women said unto Na'omi, Blessed be the Lord, who hath not allowed to be wanting unto thee a kinsman this day: and may his name become famous in Israel.
15 Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
And may he be unto thee one who refresheth thy soul, and who nourisheth thy old age; for thy daughter-in-law, who loveth thee, hath born him, she who is better to thee than seven sons.
16 Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
And Na'omi took the child, and laid it in her lap, and she became a nurse unto it.
17 Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
And the neighboring women gave him a name, saying, There hath been a son born unto Na'omi: and they called his name 'Obed, who is the father of Jesse, the father of David.
18 Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
And these are the generations of Perez: Perez begat Chezron;
19 Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
And Chezron begat Ram; and Ram begat 'Amminadab;
20 Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
And 'Amminadab begat Nachshon; and Nachshon begat Salmah;
21 Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
And Salmon begat Bo'az; and Bo'az begat 'Obed;
22 Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.
And 'Obed begat Jesse, and Jesse begat David.

< Rut 4 >