< Rut 3 >

1 Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
Et Naomi, sa belle-mère, lui dit: Ma fille, ne te chercherai-je pas un asile, afin que tu sois heureuse?
2 Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
Et maintenant, Booz, avec les servantes de qui tu as été, n'est-il pas notre parent? Voici, il vannera cette nuit les orges qui sont dans son aire.
3 Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
Lave-toi, et oins-toi, et mets sur toi ton manteau, et descends dans l'aire; mais ne te fais point connaître à cet homme, jusqu'à ce qu'il ait achevé de manger et de boire.
4 Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
Et quand il se couchera, sache le lieu où il couche, puis entre, et découvre ses pieds, et te couche; alors il te dira ce que tu auras à faire.
5 Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
Et elle lui répondit: Je ferai tout ce que tu me dis.
6 Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
Elle descendit donc à l'aire, et fit tout ce que sa belle-mère lui avait commandé.
7 Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
Et Booz mangea et but, et son cœur fut heureux, et il vint se coucher au bout d'un tas de gerbes. Alors elle vint tout doucement, et découvrit ses pieds, et se coucha.
8 Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
Et au milieu de la nuit, cet homme-là eut peur; il se pencha, et voici, une femme était couchée à ses pieds.
9 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
Alors il lui dit: Qui es-tu? Et elle répondit: Je suis Ruth, ta servante. Étends le pan de ta robe sur ta servante; car tu as droit de rachat.
10 Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
Et il dit: Ma fille, que l'Éternel te bénisse! Cette dernière bonté que tu me témoignes est plus grande que la première, de n'être point allée après les jeunes gens, pauvres ou riches.
11 Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
Maintenant donc, ma fille, ne crains point, je ferai pour toi tout ce que tu me diras; car toute la porte de mon peuple sait que tu es une femme vertueuse.
12 Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
Et maintenant, il est très vrai que j'ai droit de rachat; mais il y en a un autre, qui est plus proche que moi.
13 Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
Passe ici cette nuit; et, au matin, si cet homme veut user du droit de rachat envers toi, à la bonne heure, qu'il en use; mais s'il ne lui plaît pas de te racheter, moi je te rachèterai; l'Éternel est vivant! Reste couchée jusqu'au matin.
14 Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
Elle demeura donc couchée à ses pieds, jusqu'au matin; et elle se leva avant qu'on pût se reconnaître l'un l'autre. Et Booz dit: Qu'on ne sache pas qu'une femme est entrée dans l'aire.
15 Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
Il lui dit encore: Donne-moi le manteau qui est sur toi, et tiens-le. Et elle le tint, et il mesura six mesures d'orge, qu'il chargea sur elle; puis il rentra dans la ville.
16 Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
Puis Ruth revint chez sa belle-mère, qui lui dit: Qui es-tu, ma fille? Et elle lui déclara tout ce que cet homme avait fait pour elle.
17 ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
Et elle dit: Il m'a donné ces six mesures d'orge; car il m'a dit: Tu ne retourneras point à vide auprès de ta belle-mère.
18 Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”
Et Naomi dit: Ma fille, reste ici jusqu'à ce que tu saches comment la chose tournera; car cet homme ne se donnera point de repos qu'il n'ait aujourd'hui achevé cette affaire.

< Rut 3 >