< Rut 3 >
1 Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
And she said to her Naomi mother-in-law her O daughter my ¿ not will I seek for you a resting place that it will go well for you.
2 Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
And therefore ¿ not [is] Boaz relative our whom you were with female servants his there! he [will be] winnowing [the] threshing floor of the barley this night.
3 Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
And you will wash - and you will anoint yourself and you will put (garments your *Q(K)*) on yourself (and you will go down *Q(K)*) the threshing floor may not you make yourself known to the man until finishes he to eat and to drink.
4 Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
And let it be when lies down he and you will take note of the place where he will lie down there and you will go and you will uncover feet his (and you will lie down *Q(k)*) and he he will tell to you [that] which (you will do! *L(abh)*)
5 Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
And she said to her all that (you are saying to me *Q(K)*) I will do.
6 Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
And she went down the threshing floor and she did according to all that she had commanded her mother-in-law her.
7 Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
And he ate Boaz and he drank and it was good heart his and he went to lie down at [the] end of the heap and she came in secrecy and she uncovered feet his and she lay down.
8 Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
And it was in [the] middle of the night and he trembled the man and he twisted and there! a woman [was] lying down feet his.
9 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
And he said who? [are] you and she said I [am] Ruth maidservant your and you will spread out skirt your over maidservant your for [are] a kinsman-redeemer you.
10 Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
And he said [be] blessed you by Yahweh O daughter my you have made good loyalty your latter more than former to not to go after the young men whether poor and or rich.
11 Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
And therefore O daughter my may not you fear all that you are saying I will do for you for [is] knowing all [the] gate of people my that [are] a woman of ability you.
12 Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
And therefore for truly that (*Q(K)*) [am] a kinsman-redeemer I and also there [is] a kinsman-redeemer near more than I.
13 Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
Stay - this night and it will be in the morning if he will redeem you good let him redeem and if not he will be willing to redeem you and I will redeem you I [by] [the] life of Yahweh lie down until the morning.
14 Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
And she lay down (feet his *Q(K)*) until the morning and she arose (before *Q(K)*) he recognized anyone neighbor his and he said may not it be known that she came the woman the threshing floor.
15 Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
And he said give the shawl which [is] on you and take hold on it and she took hold on it and he measured out six barley and he put [it] on her and he came the city.
16 Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
And she came to mother-in-law her and she said who? [are] you O daughter my and she told to her all that he had done for her the man.
17 ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
And she said [the] six the barley these he gave to me for (he said to me *Q(K)*) may not you go empty to mother-in-law your.
18 Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”
And she said sit down O daughter my until that you will know! how? will it fall out a matter for not he will be at peace the man that except he has finished the matter this day.