< Rut 3 >

1 Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
Naomi her mother-in-law said to her, "My daughter, shall I not seek rest for you, that it may be well with you?
2 Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
Now isn't Boaz our kinsman, with whose maidens you were? Look, he winnows barley tonight at the threshing floor.
3 Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
Therefore wash yourself, anoint yourself, and put on your clothes, and go down to the threshing floor, but do not make yourself known to the man until he has finished eating and drinking.
4 Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
It shall be, when he lies down, that you shall notice the place where he lies, and you shall go in, and uncover his feet, and lie down; then he will tell you what you shall do."
5 Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
She said to her, "All that you say I will do."
6 Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
She went down to the threshing floor, and did according to all that her mother-in-law told her.
7 Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
When Boaz had eaten and drank, and his heart was merry, he went to lie down at the end of the heap of grain. She came quietly, uncovered his feet, and lay down.
8 Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
It happened at midnight, that the man was startled and turned over; and look, a woman lay at his feet.
9 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
He said, "Who are you?" She answered, "I am Ruth your handmaid. Therefore spread the corner of your garment over your handmaid; for you are a redeeming kinsman."
10 Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
He said, "Blessed are you by the LORD, my daughter. You have shown more kindness in the latter end than at the beginning, inasmuch as you didn't follow young men, whether poor or rich.
11 Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
Now, my daughter, do not be afraid; I will do to you all that you say; for all the city of my people does know that you are a worthy woman.
12 Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
Now it is true that I am a redeeming kinsman; however there is a redeemer closer than I am.
13 Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
Stay this night, and it shall be in the morning, that if he will perform for you the part of a redeemer, well; let him do the redeemer's part. But if he will not do the part of a redeemer for you, then I will do the part of a redeemer for you, as the LORD lives. Lie down until the morning."
14 Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
She lay at his feet until the morning. She rose up before one could discern another. For he said, "Let it not be known that the woman came to the threshing floor."
15 Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
He said, "Bring the cloak that is on you, and hold it." She held it; and he measured six measures of barley, and laid it on her; and he went into the city.
16 Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
When she came to her mother-in-law, she said, "How did it go, my daughter?" She told her all that the man had done to her.
17 ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
She said, "He gave me these six measures of barley; for he said to me, 'Do not go empty-handed to your mother-in-law.'"
18 Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”
Then she said, "Wait, my daughter, until you know how the matter will fall; for the man will not rest, until he has finished the thing this day."

< Rut 3 >