< Rut 3 >
1 Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
And Naomi her mother-in-law said to her, My daughter, shall I not seek rest for thee, that it may be well with thee?
2 Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
And now is not Boaz our kinsman, with whose maidens thou were? Behold, he winnows barley tonight in the threshing-floor.
3 Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
Wash thyself therefore, and anoint thee, and put thy raiment upon thee, and get thee down to the threshing-floor. But do not make thyself known to the man until he shall have done eating and drinking.
4 Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
And it shall be, when he lies down, that thou shall notice the place where he shall lie. And thou shall go in, and uncover his feet, and lie thee down. And he will tell thee what thou shall do.
5 Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
And she said to her, All that thou say I will do.
6 Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
And she went down to the threshing-floor, and did according to all that her mother-in-law bade her.
7 Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
And when Boaz had eaten and drunk, and his heart was merry, he went to lie down at the end of the heap of grain. And she came softly, and uncovered his feet, and laid down.
8 Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
And it came to pass at midnight, that the man was startled, and turned himself, and, behold, a woman lay at his feet.
9 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
And he said, Who are thou? And she answered, I am Ruth thy handmaid. Spread therefore thy skirt over thy handmaid, for thou are a near kinsman.
10 Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
And he said, Blessed be thou of Jehovah, my daughter. Thou have shown more kindness in the latter end than at the beginning, inasmuch as thou did not follow young men, whether poor or rich.
11 Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
And now, my daughter, fear not. I will do to thee all that thou say, for all the city of my people know that thou are a worthy woman.
12 Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
And now it is true that I am a near kinsman. However there is a kinsman nearer than I.
13 Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
Remain this night, and it shall be in the morning that if he will perform to thee the part of a kinsman, well; let him do the kinsman's part. But if he will not do the part of a kinsman to thee, then I will do the part of a kinsman to thee, as Jehovah lives. Lie down until the morning.
14 Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
And she lay at his feet until the morning. And she rose up before one could discern another. For he said, Let it not be known that the woman came to the threshing-floor.
15 Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
And he said, Bring the mantle that is upon thee, and hold it. And she held it, and he measured six measures of barley, and laid it on her, and he went into the city.
16 Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
And when she came to her mother-in-law, she said, Who are thou, my daughter? And she told her all that the man had done to her.
17 ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
And she said, He gave me these six measures of barley, for he said, Go not empty to thy mother-in-law.
18 Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”
Then she said, Sit still, my daughter, until thou know how the matter will fall, for the man will not rest until he has finished the thing this day.