< Rut 2 >

1 To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
И бе муж знаемый мужу Ноемминю: муж же силен от рода Елимелехова, имя же ему Вооз.
2 Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
И рече Руфь Моавитиня к Ноеммини: да иду убо на ниву и соберу класы вследствующи, идеже аще обрящу благодать пред очима его. Рече же ей: иди, дщи (моя).
3 Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
И иде, и пришедши собираше на ниве вследствующи жателем: и прииде по случаю в часть нивы Воозовы, иже от сродства Елимелехова.
4 Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
И се, Вооз прииде от Вифлеема и рече жнущым: Господь с вами. И реша ему: да благословит тя Господь.
5 Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
И рече Вооз отроку своему стоящему над жатели: чия отроковица сия?
6 Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
И отвеща отрок стояй над жнущими, и рече: отроковица Моавитиня есть, пришедшая с Ноемминою от села Моавля:
7 Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
и рече: да соберу ныне и сложу в снопех по следу жнущих: и прииде, и ста от утра даже и до вечера, и ни мало почи на ниве.
8 Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
И рече Вооз к Руфе: слыши, дщи, не ходи собирати на ниву ину, и ты да не отидеши отсюду: но зде прилепися ко отроковицам моим,
9 Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
и очи твои да будут на ниве, идеже жнут, и да ходиши вслед их: се, заповедах отроком не коснутися тебе: и егда возжаждеши, и да идеши к сосудом, и пиеши отнюдуже черплют отроцы.
10 Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
И паде (отроковица) ниц и поклонися до земли, и рече ему: что яко обретох благодать пред очима твоима, еже познати мя, аз же есмь странна?
11 Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
И отвеща Вооз и рече к ней: возвещением возвестися мне, елика сотворила еси со свекровию твоею по умертвии мужа твоего, и како оставила еси отца твоего и матерь твою и землю рождения твоего, и пришла еси в люди, ихже не ведала от вчера и третияго дне:
12 Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
да воздаст Господь дело твое, и да будет мзда твоя исполнь от Господа Бога Израилева, к Немуже пришла еси уповати под крилома Его.
13 Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
Она же рече: обретох благодать пред очима твоима, господине мой, яко утешил мя еси, и яко глаголал еси в сердце рабы твоея, и се, аз буду яко едина от рабынь твоих.
14 A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
И рече ей Вооз: уже час ясти, приближися убо семо, да яси хлеб мой, и омочи укрух твой во оцет. И сяде Руфь от страны жателей: и подаде ей Вооз пряжмо, и яде и насытися, и оста:
15 Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
и воста собирати. И заповеда Вооз отроком своим, глаголя: среде снопов да собирает, и не посрамите ю:
16 Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
и носяще носите ей, и отлагающе отлагайте ей от снопов, и оставите ю собирати и ясти, и не возбраните ей.
17 Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
И собира до вечера на ниве, и измлати еже собра, и бысть яко ифи мера ячменя:
18 Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
и взя, и прииде во град. И виде свекровь ея еже собра: и иземши Руфь от недр своих, даде свекрови своей, еже оставила, от нихже насытися.
19 Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
И рече к ней свекровь ея: где еси собирала днесь, и где работала? Да будет благословен познавый тя. И поведа Руфь свекрови своей, где работала, и рече: имя мужу Вооз, у негоже работах днесь.
20 Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
Рече же Ноемминь снохе своей: благословен есть Господем, яко не остави милости своея с живыми и со умершими. И рече ей Ноемминь: ужик есть нам муж той, и есть от ужик наших.
21 Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
И рече Руфь ко свекрови своей: и мне убо рече: ко отроковицам моим пристани, дондеже скончают всю жатву, яже есть мне.
22 Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
И рече Ноемминь к Руфе снохе своей: благо, дщи, яко ходила еси со отроковицами его, и не сопротивятся тебе на иней ниве.
23 Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.
И приста Руфь ко отроковицам Воозовым собирати (класы), дондеже скончася жатва ячменя и пшеницы: и седе со свекровию своею.

< Rut 2 >