< Rut 2 >

1 To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
Or le mari de Nahomi avait là un parent, homme fort et vaillant, de la famille d'Eli-mélec, qui avait nom Booz.
2 Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
Et Ruth la Moabite dit à Nahomi: Je te prie que j'aille aux champs, et je glanerai quelques épis après celui devant lequel j'aurai trouvé grâce. Et elle lui répondit: Va, ma fille.
3 Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
Elle s'en alla donc et entra dans un champ, et glana après les moissonneurs; et il arriva qu'elle se rencontra dans un champ qui appartenait à Booz, lequel [était] de la famille d'Eli-mélec.
4 Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
Or voici, Booz vint de Bethléhem, et il dit aux moissonneurs: L'Eternel soit avec vous; et ils lui répondirent: L'Eternel te bénisse.
5 Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
Puis Booz dit à son serviteur qui avait charge sur les moissonneurs: A qui est cette jeune fille?
6 Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
Et le serviteur qui avait charge sur les moissonneurs, répondit, et dit: C'est une jeune femme Moabite, qui est venue avec Nahomi du pays de Moab.
7 Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
Et elle nous a dit: Je vous prie que je glane, et que j'amasse quelques poignées après les moissonneurs; étant donc entrée elle est demeurée depuis le matin jusqu'à cette heure. C'est là le peu de temps qu'elle a demeuré en la maison.
8 Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
Alors Booz dit à Ruth: Ecoute, ma fille: ne va point glaner dans un autre champ, et même ne sors point d'ici; et ne bouge point d'ici d'auprès de mes jeunes filles.
9 Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
Regarde le champ où l'on moissonnera, et va après elles; n'ai-je pas défendu à mes garçons de te toucher? et si tu as soif, va aux vaisseaux, et bois de ce que les garçons auront puisé.
10 Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
Alors elle tomba le visage contre terre, et se prosterna, et lui dit: Comment ai-je trouvé grâce devant toi, que tu me connaisses, vu que je suis étrangère?
11 Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
Booz répondit, et lui dit: Tout ce que tu as fait à ta belle-mère, depuis que ton mari est mort, m'a été exactement rapporté; [et] comment tu as laissé ton père, et ta mère, et le pays de ta naissance, et tu es venue vers un peuple que tu n'avais point connu auparavant.
12 Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
L'Eternel récompense ton œuvre, et que ton salaire soit entier de la part de l'Eternel le Dieu d'Israël, sous les ailes duquel tu t'es venue retirer.
13 Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
Et elle dit: Monseigneur, je trouve grâce devant toi, car tu m'as consolée, et tu as parlé selon le cœur de ta servante; et cependant je ne suis point autant que l'une de tes servantes.
14 A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
Booz lui dit encore à l'heure du repas: Approche-toi d'ici, et mange du pain, et trempe ton morceau dans le vinaigre; et elle s'assit à côté des moissonneurs, et il lui donna du grain rôti, et elle en mangea, et fut rassasiée, et serra le reste.
15 Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
Puis elle se leva pour glaner; et Booz commanda à ses garçons, en disant: Qu'elle glane même entre les javelles, et ne lui faites point de honte.
16 Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
Et même vous lui laisserez, comme par mégarde, quelques poignées; vous les lui laisserez, et elle les recueillera, et vous ne [l'en] censurerez point.
17 Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
Elle glana donc au champ jusqu'au soir, et elle battit ce quelle avait recueilli, et il y eut environ un Epha d'orge.
18 Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
Et elle l'emporta, et vint en la ville; et sa belle-mère vit ce qu'elle avait glané. Elle tira aussi ce qu'elle avait serré de ce qu'elle avait eu de reste après qu'elle eut été rassasiée, et elle le lui donna.
19 Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
Alors sa belle-mère lui dit: Où as-tu glané aujourd'hui, et où as-tu fait [ceci]? Béni soit celui qui t'a reconnue. Et elle déclara à sa belle-mère chez qui elle avait fait cela, et dit: L'homme chez qui j'ai fait ceci aujourd'hui, s'appelle Booz.
20 Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
Et Nahomi dit à sa belle-fille: Béni soit-il de l'Eternel, puisqu'il a la même bonté pour les vivants [qu'il avait eue] pour les morts. Et Nahomi lui dit: Cet homme nous est proche parent, et il est un de ceux qui ont le droit de retrait lignager.
21 Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
Et Ruth la Moabite dit: Et même il m'a dit: Ne bouge point d'avec les garçons qui m'appartiennent, jusqu'à ce qu'ils aient achevé toute la moisson qui m'appartient.
22 Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
Et Nahomi dit à Ruth sa belle-fille: Ma fille, il est bon que tu sortes avec ses jeunes filles, et qu'on ne te rencontre point dans un autre champ.
23 Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.
Elle ne bougea donc point d'avec les jeunes filles de Booz, afin de glaner, jusqu'à ce que la moisson des orges et la moisson des froments fût achevée, puis elle se tint avec sa belle-mère.

< Rut 2 >