< Rut 2 >

1 To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
Or, Noémi se connaissait un parent de son mari, un homme considérable par sa richesse, de la famille d’Elimélec, et qui se nommait Booz.
2 Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
Ruth la Moabite dit un jour à Noémi: "Je voudrais aller dans les champs glaner des épis à la suite de celui qui me ferait bon accueil." Noémi lui répondit: "Va, ma fille."
3 Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
Elle alla donc et s’en vint glaner dans un champ derrière les moissonneurs; le hasard l’avait conduite dans une pièce de terre appartenant à Booz, de la famille d’Elimélec.
4 Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
Voilà que Booz arrivait justement de Bethléem; il dit aux moissonneurs: "Que le Seigneur soit avec vous!" Et eux de répliquer: "Le Seigneur te bénisse!"
5 Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
Booz demanda à son serviteur qui dirigeait les moissonneurs: "A qui cette jeune fille?"
6 Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
Le serviteur chargé de surveiller les moissonneurs répondit: "C’Est une jeune fille moabite, celle qui est venue avec Noémi des plaines de Moab.
7 Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
Elle nous a dit: Je voudrais glaner et recueillir des épis près des tas de gerbes, à la suite des moissonneurs. Ainsi elle est venue, et elle se trouve ici depuis le matin jusqu’à présent, tant son séjour à la maison a été de courte durée."
8 Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
Booz dit alors à Ruth: "Entends-tu, ma fille, ne va pas glaner dans un autre champ, et ne t’éloigne pas d’ici; attache-toi de la sorte aux pas de mes jeunes servantes.
9 Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
Aie les yeux fixés sur le champ qu’elles moissonneront et marche à leur suite; j’ai bien recommandé aux jeunes gens de ne pas te molester; si tu as soif, va où sont les vases et bois de ce que les jeunes gens auront puisé."
10 Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
Ruth se jeta la face contre terre, se prosterna et lui dit: "Comment ai-je pu trouver grâce à tes yeux, pour que tu t’intéresses à moi, qui suis une étrangère?"
11 Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
Booz lui répliqua en disant: "On m’a fidèlement rapporté tout ce que tu as fait pour ta belle-mère après la mort de ton mari: que tu as quitté ton père, ta mère et ton pays natal pour te rendre auprès d’un peuple que tu ne connaissais ni d’hier ni d’avant-hier.
12 Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
Que l’Eternel te donne le prix de ton œuvre de dévouement! Puisses-tu recevoir une récompense complète du Seigneur, Dieu d’Israël, sous les ailes duquel tu es venue t’abriter!"
13 Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
Elle dit: "Puissé-je toujours trouver grâce à tes yeux, seigneur, car tu m’as consolée, et tes paroles sont allées au cœur de ta servante, bien que je ne sois pas même autant qu’une de tes servantes!"
14 A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
A l’heure du repas, Booz lui dit: "Approche et mange de nos aliments; tu peux aussi tremper ton pain dans le vinaigre"; elle s’assit à côté des moissonneurs, il lui offrit du grain grillé, elle en mangea à satiété et en eut encore de reste.
15 Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
Puis elle se releva pour glaner, et Booz fit cette recommandation à ses gens: "Laissez-la glaner même entre les gerbes, et ne l’humiliez pas.
16 Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
Ayez même soin de laisser tomber de vos javelles des épis que vous abandonnerez, pour qu’elle les ramasse; gardez-vous de lui parler avec dureté."
17 Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
Elle glana de la sorte dans le champ jusqu’au soir, et, lorsqu’elle eut battu ce qu’elle avait ramassé, il y avait environ un êpha d’orge.
18 Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
Elle l’emporta, rentra en ville, et sa belle-mère vit ce qu’elle avait ramassé. Ruth montra aussi et lui donna ce qu’elle avait mis en réserve après avoir mangé à sa faim.
19 Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
Sa belle-mère lui demanda: "Où donc as-tu glané aujourd’hui? Où as-tu travaillé? Béni soit celui qui t’a témoigné de la bienveillance!" Ruth fit connaître à sa belle-mère chez qui elle avait fait sa besogne: "L’Homme, dit-elle, chez qui j’ai travaillé aujourd’hui se nomme Booz."
20 Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
Alors Noémi dit à sa bru: "Béni soit-il par l’Eternel, puisqu’il n’a cessé d’être bon pour les vivants et pour les Morts!" Noémi lui dit encore: "Cet homme nous touche de près: il est de nos parents."
21 Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
Ruth la Moabite dit: "Il m’a même adressé ces mots: Attache-toi aux pas de mes gens, jusqu’à ce qu’ils aient achevé toute ma moisson."
22 Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
Et Noémi dit à Ruth, sa bru: "Il vaut bien mieux, ma fille, que tu ailles avec ses servantes; ainsi tu ne seras pas exposée à être mal accueillie dans un autre champ."
23 Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.
Ruth resta donc avec les servantes de Booz pour glaner jusqu’à l’achèvement de la moisson de l’orge et du froment; et elle continuait à habiter avec sa belle-mère.

< Rut 2 >