< Rut 2 >
1 To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
Forsothe a myyti man and a man `of grete richessis, `Booz bi name, `was kynysman of Elymelech.
2 Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
And Ruth of Moab seide to hir modir in lawe, If thou comaundist, Y schal go in to the feeld, and Y schal gadere eeris of corn that fleen the hondis of reperis, where euer Y schal fynde grace of an hosebonde man merciful in me. To whom sche answeride, Go, my douyter.
3 Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
Therfor `sche yede, and gaderide eeris of corn after the backis of reperis. Forsothe it bifelde, that `thilke feeld hadde a lord, Booz bi name, that was of the kynrede of Elymelech.
4 Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
And lo! he cam fro Bethleem. And he seide to the reperis, The Lord be with you. Whiche answeriden to hym, The Lord blesse thee.
5 Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
And Booz seide to the yong man that was souereyn to the reperis, Who is this damysel?
6 Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
Whiche answeride, This is the womman of Moab, that cam with Noemy fro the cuntrey of Moab; and sche preiede,
7 Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
that sche schulde gedere eeris of corn leeuynge bihynde, and sue the `steppis of reperis; and fro the morewtid til now sche stondith in the feeld, and sotheli nethir at a moment sche turnede ayen hoom.
8 Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
And Booz seide to Ruth, Douytir, here thou; go thou not in to anothir feelde to gadere, nether go awei fro this place, but be thou ioyned to my dameselis,
9 Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
and sue thou where thei repen; for Y comaundide to my children, that `no man be diseseful to thee; but also if thou thirstist, go to the fardels, and drynke `watris, of whiche my children drynken.
10 Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
And sche felde on hir face, and worschipide on the erthe; and seide to hym, Wherof is this to me, that Y schulde fynde grace bifor thin iyen, that thou woldist knowe me a straunge womman?
11 Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
To whom he answeride, Alle thingis ben teld to me, whiche thou didist to thi modir in lawe after the deeth of thin hosebonde, and that thou hast forsake thi fadir and modir, and the lond `in which thou were borun, and hast come to a puple, whom thou `knowist not bifore.
12 Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
The Lord yelde to thee for thi werk, and resseyue thou ful mede of the Lord God of Israel, to whom thou camest, and vndir whose wengis thou fleddist.
13 Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
And sche seide, My lord, Y haue founde grace bifor thin iyen, which hast coumfortid me, and hast spoke to the herte of thin handmaide, which am not lijk oon of thi damesels.
14 A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
And Booz seide to hir, Whanne the our of etyng is, come thou hidur, and ete breed, and wete thi mussel in vynegre. Therfor sche sat at the `side of reperis; and he dresside to hir potage, and sche eet, and was fillid; and sche took the relifs.
15 Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
And sche roos fro thennus to gadere eeris of corn bi custom. Forsothe Booz comaundide to hise children, and seide, Also if sche wole repe with you,
16 Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
forbede ye not hir, and also `of youre handfuls caste ye forth of purpos, and suffre ye to abide, that sche gadere with out schame; and no man repreue hir gaderynge.
17 Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
Therfor sche gaderide in the feeld `til to euentid; and sche beet with a yerde, and schook out tho thingis that sche hadde gaderid; and sche foond of barly as the mesure of ephi, that is, thre buschels.
18 Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
Which sche bar, and turnede ayen in to the citee, and schewide to hir modir in lawe; ferthermore sche brouyte forth, `and yaf to hir the relifs of hir mete, with which mete sche was fillid.
19 Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
And the modir in lawe seide to hir, Where `gaderidist thou to dai, and where `didist thou werk? Blessid be he, that hadde mercy on thee. And sche telde to hir, at whom sche wrouyte; and sche seide the name `of the man, that he was clepid Booz.
20 Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
To whom Noemy answeride, Blessid be he of the Lord, for he kepte also to deed men the same grace, which he yaf to the quike. And eft sche seide, He is oure kynysman.
21 Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
And Ruth seide, Also he comaundide this to me, that so longe Y schulde be ioyned to hise reperis, til alle the cornes weren repid.
22 Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
To whom hir modir in lawe seide, My douyter, it is betere that thou go `out to repe with hise damysels, lest in another feeld ony man ayenstonde thee.
23 Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.
`Therfor sche was ioyned to the damesels of Booz; and so longe sche rap with hem, til bothe barli and wheete weren closid in the bernys.