< Rut 1 >
1 A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
И бысть внегда судяху судии, бысть глад на земли. И иде муж от Вифлеема Иудина обитати в селе Моавли, сам и жена его, и два сыны его:
2 Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
имя же мужеви Елимелех, имя же жене его Ноемминь и имя двема сынома его Маалон и Хелеон, Ефрафейстии от Вифлеема Иудина. И приидоша в село Моавле, и беша тамо.
3 To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
И умре Елимелех муж Ноемминин, и остася она и оба сыны ея:
4 Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
и пояста себе жены Моавитския: имя единей Орфа и имя вторей Руфь: и жиша тамо до десяти лет.
5 sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
И умроста оба сыны ея, Маалон и Хелеон, и остася жена от мужа своего и от обоих сынов ея.
6 Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
И воста она и обе снохи ея, и возвратишася с села Моавля: зане услыша на селе Моавли, яко присети Господь людий Своих дати им хлебы.
7 Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
И отиде от места, идеже бе, она и обе снохи ея с нею, и идяху в путь возвратитися в землю Иудину.
8 Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
И рече Ноемминь обема снохама своима: идите убо, возвратитеся каяждо в дом отца своего: да сотворит Господь с вами милость, якоже сотвористе со умершими и со мною:
9 Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
да даст Господь Бог вам обрести покой коейждо в дому мужа своего. И целова я: они же воздвигоша гласы своя и плакашася,
10 suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
и рекоша ей: ни, но идем с тобою в люди твоя.
11 Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
И рече Ноемминь: обратитеся убо, дщери мои, вскую идете со мною? Или еще мне сынове во утробе моей, и будут вам мужи?
12 Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
Возвратитеся убо, дщери мои и отидите, яко состарехся, и не буду мужу: аще же бых и рекла, яко у мене есть надежда, да буду мужу и рожду сыны,
13 za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
вы ли пождете их, дондеже возрастут? И вы ли удержитеся, да не будете иному мужу? Ни, дщери мои, яко горько бысть мне паче вас, яко изыде на мя рука Господня.
14 A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
И воздвигоша гласы своя, и плакаша паки. И целова Орфа свекровь свою, и возвратися в люди своя, Руфь же последова ей.
15 Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
И рече Ноемминь к Руфе: се, возвратися ятровь твоя к людем своим и к богом своим, возвратися убо и ты вслед ятрове своея.
16 Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
И рече Руфь: не срящи мене то, еже оставити тебе или обратитися мне от тебе, но идеже идеши ты, и аз пойду, и идеже водворишися ты, водворюся и аз: людие твои людие мои, и Бог твой Бог мой:
17 Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
и идеже аще умреши, умру и тамо погребуся: тако да сотворит мне Господь, и сия да приложит, яко смерть разлучит между мною и тобою.
18 Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
Видевши же Ноемминь, яко укрепися она ити с нею, умолче глаголати к ней ктому.
19 Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
Идосте же обе, дондеже приидосте в Вифлеем. И бысть егда приидосте они в Вифлеем, и возгласи весь град о них, и рекоша: еда сия есть Ноемминь?
20 Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
И рече к ним: не зовите убо мене Ноемминь, но зовите мене Горька: яко исполни мя горести Вседержитель зело:
21 In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
аз исполнь отидох, и ныне тщу мя возврати Господь: и вскую мя нарицаете Ноемминь, Господь смири мя и Вседержитель озлоби мя?
22 Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.
И возвратися Ноемминь и Руфь Моавитиня сноха ея с нею, обращающыяся с села Моавля: и приидосте в Вифлеем в начале жатвы ячменя.