< Romawa 1 >
1 Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
Paulus, Jesu Christi tjenare, kallad till Apostel, afskild till att predika Guds Evangelium;
2 Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
Hvilket han tillförene utlofvat hafver, genom sina Propheter i den Helga Skrift,
3 game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
Om sin Son, den född är af Davids säd, efter köttet;
4 Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
Hvilken är krafteliga bevisad Guds Son, efter Andan som helgar, deraf att han stod upp ifrå de döda, nämliga Jesus Christus, vår Herre;
5 Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
Genom hvilken vi hafve fått nåd, och Apostlaämbete, till att upprätta trones lydno ibland alla Hedningar, i hans Namn;
6 Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
Ibland hvilka I ock ären kallade af Jesu Christo;
7 Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Allom dem som i Rom äro, Guds kärestom, kalladom heligom. Nåd vare med eder, och frid af Gudi vårom Fader, och Herranom Jesu Christo.
8 Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
I förstone tackar jag min Gud, gjenom Jesum Christum, för eder alla, att i hela verldene talas om edra tro.
9 Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
Ty Gud är mitt vittne, hvilkom jag tjenar i minom anda, uti Evangelio som är om hans Son, att jag utan återvändo tänker på eder;
10 cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
Bedjandes alltid i mina böner, att jag dock någon tid måtte få en lyckosam väg, om Gud ville, till att komma till eder.
11 Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
Ty jag åstundar se eder, på det jag måtte några andeliga gåfvo dela med eder, till att styrka eder;
12 wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
Det är, att jag, samt med eder, måtte få hugsvalelse, genom begges våra tro, edra och mina.
13 Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
Jag vill icke dölja för eder, bröder, att jag hafver ofta haft i sinnet komma till eder, ändock jag hafver varit förhindrad allt härtill; på det jag måtte ock någon frukt skaffa ibland eder, såsom ibland andra Hedningar.
14 Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
Jag är pligtig både Greker och Barbarer, både visa och ovisa.
15 Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
Derföre, så mycket mig står till görandes, är jag redebogen att jag ock predikar eder Evangelium, som i Rom ären.
16 Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
Ty jag skämmes icke vid Christi Evangelium; ty det är Guds kraft allom dem till salighet som tro; Judomen först, så ock Grekomen;
17 Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
Derföre att derutinnan varder Guds rättfärdighet uppenbar, af tro i tro; som skrifvet är: Den rättfärdige skall lefva af sine tro.
18 Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
Ty Guds vrede af himmelen varder uppenbar öfver alla menniskornas ogudaktighet och orättfärdighet, de der förhålla sanningena i orättfärdighet.
19 gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
Ty det, som förstås kan om Gud, är dem uppenbart; ty Gud hafver dem det uppenbarat;
20 Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios )
Dermed att hans osynliga väsende, och hans eviga kraft och Gudom varder beskådad, när de besinnas af gerningarna, nämliga af verldenes skapelse; så att de äro utan ursäkt; (aïdios )
21 Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
Medan de förstodo Gud, och hafva icke prisat honom som en Gud, och ej heller tackat; utan vordo fåfängelige i sina tankar, och deras oförnuftiga hjerta är vordet mörkt.
22 Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
Då de höllo sig för visa, äro de vordne dårar;
23 suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
Och hafva förvandlat dens oförgängeliga Guds härlighet uti beläte, det ej allenast gjordt var efter förgängeliga menniskors, utan jemväl efter foglars, och fyrafött och krypande djurs liknelse.
24 Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
Derföre hafver ock Gud öfvergifvit dem i deras hjertans lustar, uti orenlighet, till att skämma sin lekamen inbördes;
25 Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn )
Hvilke förvandlat hafva Guds sanning i lögn; och hafva ärat och dyrkat de ting, som skapad äro, öfver honom som dem skapat hafver, hvilken är välsignad evinnerliga. Amen. (aiōn )
26 Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
Derföre hafver ock Gud öfvergifvit dem i skamliga lustar; ty deras qvinnor hafva förvandlat den naturliga brukningena uti den, som är emot naturen.
27 Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
Sammaledes ock männerna hafva öfvergifvit den naturliga qvinnones brukning, och hafva brunnit i sin lusta till hvarannan; man med man bedrifvit slemhet, och fått, som tillbörligit var, deras villos rätta lön i sig sjelfvom.
28 Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
Och såsom de intet aktade hafva Gud i känslo, hafver Gud öfvergifvit dem i ett vrångt sinne, till att bedrifva obeqvämlig ting;
29 Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
Fulle med all orättfärdighet, boleri, arghet, girighet, ondsko; fulle med afund, mord, kif, svek, otukt;
30 da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
Örnatasslare, bakdantare, Guds föraktare, våldsverkare, högfärdige, stolte, illfundige, föräldromen olydige;
31 su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
Oförnuftige, ordlöse, okärlige, trolöse, obarmhertige;
32 Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.
Hvilke, ändå de Guds rättviso veta, att de som sådant göra äro värde döden, likväl göra de det icke allenast, utan ock hålla med dem som det göra.