< Romawa 1 >
1 Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
Paul, a servant of Jesus Christ, called an apostle, having been separated unto the gospel of God,
2 Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
which He proclaimed beforehand through His prophets in the holy scriptures,
3 game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
concerning his Son, having been born of the seed of David according to the flesh;
4 Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
having been ordained the Son of God with power, according to the spirit of holiness, from the resurrection of the dead, of Jesus Christ our Lord:
5 Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
through whom we received grace and apostleship, unto obedience of faith among all the Gentiles, in behalf of his name:
6 Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
among whom ye are also called of Jesus Christ:
7 Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
to all the beloved of God who are in Rome, saints having been called. Grace and peace to you from God our Father and the Lord Jesus Christ.
8 Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
In the first place, indeed, I praise my God through Jesus Christ for you all, because your faith is spoken of throughout the whole world.
9 Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
For God is my witness, whom I serve in my spirit in the gospel of his Son, how I unceasingly make mention of you always in my prayer;
10 cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
praying, if by any means I shall be prospered in the will of God to come to you.
11 Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
For I long to see you, in order that I may impart unto you a certain spiritual grace, that you may be established;
12 wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
but this is the consolation among you through faith in one another, both of you and me.
13 Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
But I do not wish you to be ignorant, brethren, that frequently I purposed to come to you, and was hindered hitherto, in order that I may have some fruit among you, as well as also among other Gentiles.
14 Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
I am debtor both to the Greeks, and to the barbarians; both to the wise, and the unwise:
15 Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
so to my utmost ability, I am ready to preach the gospel to you who are in Rome also.
16 Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
For I am not ashamed of the gospel: for it is the power of God unto salvation to every one that believeth; to the Jew first, and also to the Greek.
17 Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
For the righteousness of God is revealed in him from faith to faith: as has been written, But the just shall live by faith.
18 Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
For the wrath of God is revealed from heaven against all ungodliness and unrighteousness of men, who hold the truth in unrighteousness;
19 gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
because that which is known of God is manifest in them; for God has revealed it to them:
20 Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios )
for the invisible things of Him from the creation of the world are seen, being known by the things which are made, even His eternal power and divinity; so that they are without excuse: (aïdios )
21 Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
because, knowing God, they did not glorify Him as God, neither were they thankful; but they became vain in their reasonings, and their foolish heart was darkened.
22 Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
Saying that they were wise, they became fools,
23 suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
and changed the glory of the invisible God into the similitude of the likeness of corruptible man, and of birds, and of quadrupeds, and of creeping things.
24 Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
Therefore God gave them up, in the lusts of their hearts, to impurity, to dishonor their bodies among themselves:
25 Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn )
who changed the truth of God into a lie, and worshiped and served the creature rather than the Creator, who is blessed for evermore: amen. (aiōn )
26 Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
On account of this God gave them up to the lusts of dishonor: for indeed their women changed the natural use to that which is against nature:
27 Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
likewise also the men, having left the natural use of the woman, burned in their desire towards one another; men with men working out disgrace, and receiving the reward of their error among themselves which it behooved.
28 Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
And as they did not approve to have God in their knowledge, God gave them up to a reprobate mind, to do those things which are inappropriate;
29 Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
being filled with all injustice, wickedness, vice, covetousness; full of envy, murder, strife, deceitfulness, evil affection;
30 da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
whisperers, calumniators, haters of God, insulters, proud, arrogant, practitioners of evils, disobedient to parents,
31 su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
covenant-breakers, incontinent, without natural affections, unmerciful,
32 Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.
who, knowing the rightfulness of God, that those who do such things are worthy of death, not only do the same, but they even delight in those who are doing them.