< Romawa 9 >
1 Ina faɗin gaskiya a cikin Kiristi ba ƙarya nake yi ba, lamirina ya tabbatar da wannan a cikin Ruhu Mai Tsarki.
Resnico govorim v Kristusu, ne lažem, to mi spričuje moja vest v duhu svetem,
2 Ina da baƙin ciki mai yawa da kuma rashin kwanciyar rai marar ƙarewa a zuciyata.
Da imam veliko žalost in neprenehano bolečino v svojem srcu.
3 Gama da so na ne, sai a la’anta ni a kuma raba ni da Kiristi saboda’yan’uwana, waɗannan na kabilata,
Kajti želel bi, da bi bil sam jaz preklet od Kristusa za svoje brate, kteri so mi v rodu po mesu;
4 mutanen Isra’ila. Su ne Allah ya mai da su’ya’yansa, ya bayyana musu ɗaukakarsa, ya ba su alkawarinsa da Dokarsa, ya nuna musu hanyar sujada ta gaske, ya kuma ba su sauran alkawura.
Kteri so Izraelci, kterih je posinstvo, in slava, in zaveze, in postavodajstvo, in služba, in obljube,
5 Kakannin-kakannin nan kuma nasu ne, Kiristi kuma, ta wurin zamansa mutum, na kabilarsu ne. Yabo ya tabbata ga Allah har abada, shi da yake bisa kome! Amin. (aiōn )
Kteri so očetje, in od kterih je Kristus po mesu, kteri je Bog nad vsemi blagoslovljen na veke. Amen. (aiōn )
6 Ba cewa maganar Allah ta kāsa ba ne. Gama ba duk waɗanda suke zuriyar Isra’ila ne suke Isra’ila na gaske ba.
Ni pa tako, da je beseda Božja izgubljena, ker niso vsi ti Izraelci, kteri so od Izraela.
7 Ba kuwa don su zuriyarsa ne dukansu suka zama’ya’yan Ibrahim ba. A maimako, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
Tudi kteri so seme Abrahamovo, niso vsi otroci, nego: "Izaku se ti bo imenovalo seme."
8 Ana iya cewa zaman zuriyar Ibrahim, ba shi ne zama’ya’yan Allah ba, a’a, zuriya ta alkawarin nan su ne ake lasaftawa zuriyar Ibrahim.
To je, niso ti, kteri so otroci mesa, otroci Božji, nego otroci obljube računijo se za seme.
9 Ga yadda aka yi alkawarin nan, “A ƙayyadadden lokaci zan dawo, Saratu kuma za tă haifi ɗa.”
Kajti beseda obljube je ta: "Ta čas bom prišel in Sara bo imela sina."
10 Ba ma haka kaɗai ba,’ya’yan Rifkatu suna da mahaifi guda ne, wato, mahaifinmu Ishaku.
Pa ne samo ona, nego tudi Rebeka, z enim imajoč otroke, z Izakom očetom našim;
11 Duk da haka, tun ba a haifi tagwayen nan ba, balle su yi wani abu mai kyau ko marar kyau don nufin Allah bisa ga zaɓensa ya tabbata, ba ga aikin lada ba, sai dai ga kiransa,
Kajti ko se še nista narodila, tudi ne storila kaj dobrega ali hudega, da bi ostal sklep Božji poleg izbire,
12 ba ta wurin ayyuka ba sai dai ta wurin shi wanda ya kira, aka faɗa mata cewa, “Babban zai bauta wa ƙaramin.”
Ne za voljo del, nego za voljo tistega, kteri kliče, reklo se jej je: "Veči bo služil manjšemu."
13 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yaƙub ne na so, amma Isuwa ne na ƙi.”
Kakor je pisano: "Jakoba sem ljubil, a Ezava sovražil."
14 Me za mu ce ke nan? Allah marar adalci ne? Sam, ko kaɗan!
Kaj torej porečemo? krivica je pri Bogu? Bog ne daj!
15 Gama ya ce wa Musa, “Zan nuna jinƙai ga wanda zan nuna jinƙai, zan kuma ji tausayin wanda zan ji tausayi.”
Kajti Mojzesu govori: "Pomiloval bom, kogar pomilujem, in usmilil se ga bom, kogar se usmiljujem."
16 Saboda haka, bai danganta ga sha’awar mutum ko ƙoƙarinsa ba, sai dai ga jinƙan Allah.
To torej ni v moči ne tega, kteri hoče, ne tega, kteri ne če, nego Boga, kteri pomiluje.
17 Gama Nassi ya ce wa Fir’auna, “Na ɗaga ka saboda wannan manufa, saboda in nuna ikona a cikinka domin kuma a shaida sunana a duniya duka.”
Kajti pismo govori Faraonu: "Za to sem te obudil, da pokažem na tebi svojo moč, in da se oznani moje ime po vsej zemlji."
18 Saboda haka Allah yana nuna jinƙai ga wanda yake so, yana kuma taurara zuciyar wanda yake so.
Tako torej, kogar hoče, pomiluje, a kogar hoče, trdi.
19 Waninku zai iya ce mini, “To, don me har yanzu Allah yake ganin laifinmu? Gama wa zai iya tsayayya da nufinsa?”
Porečeš mi torej; kaj se še toži? kdo njegovej volji nasprotuje?
20 Amma wane ne kai, ya mutum, da za ka mayar wa Allah magana? “Ashe, abin da aka gina zai iya ce wa wanda ya gina shi, ‘Don me ka gina ni haka?’”
Ali kdo si ti, o človek, kteri se z Bogom pregovarjaš? poreče li izdelek izdelovalcu: za kaj si me naredil tako?
21 Ashe, mai ginin tukwane ba shi da iko yin amfani da yumɓu guda yă gina tukunya domin ayyuka masu daraja da kuma waɗansu don ayyuka marasa daraja?
Nima li oblasti lončar nad glino, da iz ravno tiste grude naredi eno posodo za čast, a drugo za nečast?
22 Haka ma aikin Allah yake. Ya so yă nuna fushinsa yă kuma sanar da ikonsa, ya yi haka cikin haƙuri ƙwarai ga waɗanda suka cancanci fushinsa, waɗanda aka shirya domin hallaka?
Če je Bog hotel pokazati jezo in razglasiti svojo moč, prenesel je v velikej potrpljivosti posode jeze pripravljene za pogubo.
23 Haka kuma ya so yă sanar da wadatar ɗaukakarsa ga waɗanda suka cancanci jinƙansa, waɗanda ya shirya tun kafin lokaci don ɗaukaka
In da bi razglasil bogastvo slave svoje na posodah usmiljenja, ktere je naprej pripravil za zlavo,
24 har da mu ma, mu da ya kira, ba daga cikin Yahudawa kaɗai ba amma har ma daga cikin Al’ummai?
Ktere nas je tudi poklical ne samo izmed Judov, nego tudi izmed poganov;
25 Kamar yadda ya faɗa a Hosiya. “Zan kira su ‘mutanena,’ su da ba mutanena ba; zan kuma kira ta ‘ƙaunatacciyata,’ ita da ba ƙaunatacciyata ba,”
(Kakor tudi pri Oseji pravi: "Imenoval bom ne moje ljudstvo svoje ljudstvo, in ne ljubico ljubico."
26 kuma, “Zai zama cewa a daidai inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba,’ za a ce da su, ‘’ya’yan Allah mai rai.’”
In bode, na mestu, kjer se jim je reklo: "Niste moj narod vi, tam se bodo imenovali sinovi Boga živega."
27 Ishaya ya ɗaga murya game da Isra’ila ya ce, “Ko da yake yawan Isra’ilawa yana kama da yashi a bakin teku, ragowa ce kaɗai za su sami ceto.
Izaija pa vpije nad Izraelom: "Ko bi bilo število sinov Izraelovih kolikor morskega peska, ostanek se bo zveličal."
28 Gama Ubangiji zai zartar da hukuncinsa a bisan duniya da sauri kuma ba da ɓata lokaci ba.”
Kajti besedo je dokončeval in skrajševal v pravici, da bo besedo skrajšano storil Gospod na zemlji."
29 Yana nan kamar yadda Ishaya ya riga ya faɗa. “Da ba don Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana zuriya ba, da mun zama kamar Sodom, da mun kuma zama kamar Gomorra.”
In kakor je najprej povedal Izaija: "Ko bi Gospod: Sabaot, ne bil pustil nam semena, kakor Sodoma bili bi postali in Gomori podobni.")
30 Me za mu ce ke nan? Ai, Al’ummai da ba su nemi adalci ba, sun same shi, adalcin da yake ta wurin bangaskiya;
Kaj torej porečemo? da so pogani, kteri niso iskali pravice, dobili pravico, ali pravico, ktera je iz vere;
31 amma Isra’ila da suka yi ƙwazo wajen bin Dokar adalci, ba su same shi ba.
A Izrael iskajoč postavo pravice na postavo pravice ni zadel?
32 Don me? Domin sun yi ƙwazo wajen binta ba ta wurin bangaskiya ba sai dai ta wurin ayyuka. Sun yi tuntuɓe a kan “dutsen sa tuntuɓe.”
Za voljo česa? ker ni iz vere, nego kakor iz del pravice; kajti spotaknili so se ob kamen spotike,
33 Kamar yadda yake a rubuce, “Ga shi, na sa dutse a Sihiyona da yake sa mutane yin tuntuɓe da kuma dutsen da yake sa su fāɗi wanda kuwa ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
Kakor je pisano: Glej, polagam v Sionu kamen spotike in skalo pohujšanja; in kdorkoli veruje v njega, osramotil se ne bo.