< Romawa 8 >
1 Saboda haka, yanzu babu hukunci don waɗanda suke cikin Kiristi Yesu,
Тож немає тепер жодного о́суду тим, хто ходить у Христі Ісусі не за тілом, а за Духом,
2 gama ta wurin Kiristi Yesu dokar Ruhu mai ba da rai ta’yantar da ni daga Dokar Musa.
бо зако́н Духа життя в Христі Ісусі визволив мене від зако́ну гріха й смерти.
3 Gama abin da dokar ba tă iya yi saboda kāsawar mutuntaka ba, Allah ya yi shi sa’ad da ya aiko da Ɗansa a kamannin mutum mai zunubi, don yă zama hadaya ta zunubi. Ta haka, ya hukunta zunubi a cikin mutum mai zunubi.
Бо що було неможливе для Закону, у чо́му був він безсилий тілом, — Бог послав Сина Свого в подобі гріховного тіла, і за гріх осудив гріх у тілі,
4 Ya yi haka domin yă cika bukatun adalcin doka a cikinmu, mu da ba ma rayuwa bisa ga mutuntaka, sai dai bisa ga Ruhu.
щоб ви́коналось ви́правдання Закону на нас, що ходимо не за тілом, а за Духом.
5 Waɗanda suke rayuwa bisa ga mutuntaka sun kafa hankulansu a kan sha’awace-shawa’acen jiki; amma waɗanda suke rayuwa bisa ga Ruhu sun kafa hankulansu a kan abubuwan da Ruhu yake so.
Бо ті, хто ходить за тілом, ду́мають про тілесне, а хто за Духом — про духовне.
6 Ƙwallafa rai ga al’amuran halin mutuntaka ƙarshensa mutuwa ne, ƙwallafa rai ga al’amuran Ruhu kuwa rai ne da salama;
Бо думка тілесна — то смерть, а думка духовна — життя та мир,
7 hankalin mai zunubi na gāba da Allah. Ba ya biyayya da dokar Allah, ba kuwa zai iya yin haka ba.
думка бо тілесна — ворожне́ча на Бога, бо не ко́риться Законові Божому, та й не може.
8 Waɗanda mutuntaka yake mulkinsu ba za su iya su gamshi Allah ba.
І ті, хто хо́дить за тілом, не можуть догодити Богові.
9 Ku kam, ana mulkinku ba ta wurin mutuntaka ba, sai dai ta wurin Ruhu, in Ruhun Allah yana zaune a cikinku. In kuma wani ba shi da Ruhun Kiristi, shi ba na Kiristi ba ne.
А ви не в тілі, але в Дусі, бо Дух Божий живе в вас. А коли хто не має Христового Духа, той не Його.
10 Amma in Kiristi yana a cikinku, jikinku matacce ne saboda zunubi, duk da haka ruhunku yana a raye saboda adalci.
А коли Христос у вас, то хоч тіло мертве через гріх, але дух живий через праведність.
11 In kuwa Ruhu wannan da ya tā da Yesu daga matattu yana zama a cikinku, shi wanda ya tā da Kiristi daga matattu zai ba da rai ga jikunanku masu mutuwa ta wurin Ruhunsa, wanda yake zama a cikinku.
А коли живе в вас Дух Того, Хто воскресив Ісуса з мертвих, то Той, хто підняв Христа з мертвих, ожи́вить і смертельні тіла ваші через Свого Духа, що живе в вас.
12 Saboda haka’yan’uwa, muna da hakki, amma ba na wanda za mu yi rayuwar mutuntaka da yake so ba.
Тому́ то, браття, ми не боржники́ тіла, щоб жити за тілом;
13 Gama in kuna rayuwa bisa ga mutuntaka, za ku mutu; amma in ta wurin Ruhu kuka kashe ayyukan jikin nan, za ku rayu.
бо коли живе́те за тілом, то маєте вмерти, а коли Духом умертвля́єте тілесні вчинки, то бу́дете жити.
14 Domin waɗanda Ruhun Allah yake bi da su ne’ya’yan Allah.
Бо всі, хто водиться Духом Божим, вони сини Божі;
15 Gama ba ku karɓi ruhun da ya mai da ku bayi da za ku sāke jin tsoro ba ne, sai dai kun karɓi Ruhun zaman ɗa. Ta wurinsa kuwa muke kira, “Abba, Uba.”
бо не взяли́ ви духа неволі знов на страх, але взяли ви Духа сині́вства, що через Нього кличемо: „Авва, Отче!“
16 Ruhu kansa yana ba da shaida tare da ruhunmu cewa mu’ya’yan Allah ne.
Сам Цей Дух сві́дчить ра́зом із духом нашим, що ми — діти Божі.
17 In kuwa mu’ya’ya ne, to, mu magāda ne, magādan Allah da kuma abokan gādo tare da Kiristi, in kuwa muna tarayya a cikin shan wuyarsa to, za mu yi tarayya a cikin ɗaukakarsa.
А коли діти, то й спадкоємці, спадкоємці ж Божі, а співспадкоємці Христові, коли тільки ра́зом із Ним ми терпимо́, щоб разом із Ним і просла́витись.
18 A ganina, wuyar da muke sha a wannan lokaci ba su isa a kwatanta da ɗaukakar da za a bayyana a cikinmu ba.
Бо я ду́маю, що страждання тепе́рішнього ча́су нічого не варті супроти тієї слави, що має з'явитися в нас.
19 Halitta tana jira da marmari ta ƙosa ta ga bayyanuwar’ya’yan Allah.
Бо чека́ння створі́ння очікує з'я́влення синів Божих,
20 Gama an sa halitta a cikin wulaƙanci, ba da son ta ba, sai dai ta wurin nufin wannan da ya mai da ita haka, da bege
бо створі́ння покорилось марно́ті не добровільно, але через того, хто скори́в його, в надії,
21 cewa za a’yantar da halitta kanta daga bautarta ga ruɓewa a kuma kawo ta cikin’yancin ɗaukakar’ya’yan Allah.
що й саме створіння ви́зволиться від неволі тління на волю слави синів Божих.
22 Mun san cewa dukan halitta tana nishi sai ka ce mace mai naƙuda har yă zuwa wannan lokaci.
Бо знаємо, що все створі́ння ра́зом зідхає й ра́зом мучиться аж досі.
23 Ba haka kaɗai ba ma, mu kanmu da muke da nunan fari na Ruhu, muna nishi a ciki-cikinmu yayinda muke jira da marmari a maishe mu’ya’yan riƙo na Allah, fansar jikunanmu.
Але не тільки воно, але й ми самі, маючи зача́ток Духа, і ми самі в собі зідхаємо, очікуючи синівства, відкуплення нашого тіла.
24 Gama a wannan begen ne muka sami ceto. Amma begen da ake gani ba bege ba ne sam. Wa yake begen abin da ya riga ya samu?
Надією бо ми спасли́ся. Надія ж, коли бачить, не є надія, бо хто що́ бачить, чому б того й наді́явся?
25 Amma in muna begen abin da ba mu riga mun samu tukuna ba, mukan jira da haƙuri.
А коли сподіва́ємось, чого не бачимо, то очікуємо того з терпеливістю.
26 Haka nan ma, Ruhu yana taimakonmu cikin rashin ƙarfinmu. Ba mu san abin da ya kamata mu roƙa cikin addu’a ba, amma Ruhu kansa yana roƙo a madadinmu da nishe-nishen da kalmomi ba sa iya bayyanawa.
Так само ж і Дух допомагає нам у наших не́мочах; бо ми не знаємо, про що маємо молитись, як належить, але Сам Дух заступається за нас невимо́вними зідха́ннями.
27 Shi kuma wanda yake binciken zukatanmu ya san halin Ruhu, domin Ruhu yana roƙo a madadin tsarkaka bisa ga nufin Allah.
А Той, Хто досліджує серця́, знає, яка думка Духа, бо з волі Божої заступається за святих.
28 Mun kuma san cewa a cikin dukan abubuwa Allah yana aikata alheri ga waɗanda suke ƙaunarsa, yana waɗanda aka kira bisa ga nufinsa.
І знаємо, що тим, хто любить Бога, хто покликаний Його постановою, усе допомагає на добре.
29 Gama waɗanda Allah ya rigyasani ya kuma ƙaddara su dace da kamannin Ɗansa, don yă zama ɗan fari cikin’yan’uwa masu yawa.
Бо кого Він передба́чив, тих і призна́чив, щоб були подібні до о́бразу Сина Його, щоб Він був перворі́дним поміж багатьма́ братами.
30 Waɗanda kuwa ya ƙaddara, su ne ya kira; waɗanda ya kira kuwa, su ne ya kuɓutar; waɗanda ya kuɓutar kuwa, su ne ya ɗaukaka.
А кого Він призначив, тих і покликав, а кого покликав, тих і ви́правдав, а кого ви́правдав, тих і просла́вив.
31 Me za mu ce ke nan game da wannan abu? In Allah yana goyon bayanmu, wa kuwa zai iya gāba da mu?
Що ж скажем на це? Коли за нас Бог, то хто проти нас?
32 Shi da bai hana Ɗansa ba, sai ma ya ba da shi saboda mu duka, ashe, ba zai kuma ba mu, tare da shi, dukan abubuwa cikin alherinsa ba?
Той же, Хто Сина Свого не пожалів, але видав Його за всіх нас, — як же не дав би Він нам із Ним і всього?
33 Wa zai kawo wani zargi a kan waɗanda Allah ya zaɓa? Allah ne mai kuɓutarwa.
Хто оска́ржувати буде Божих вибранців? Бог Той, що виправдує.
34 Wa zai yi hukunci? Yesu Kiristi ne, wanda ya mutu, fiye da haka ma, shi da aka tā da zuwa rai, yana zaune a hannun dama na Allah yana kuma yin roƙo a madadinmu.
Хто ж той, що засу́джує? Христос Ісус є Той, що вмер, надто й воскрес, — Він право́руч Бога, і Він і заступається за нас.
35 Wane ne zai raba mu da ƙaunar Kiristi? Masifa ce ko wahala ko tsanani ko yunwa ko tsiraici ko hatsari ko takobi?
Хто нас розлучить від любови Христової? Чи недоля, чи утиск, чи переслі́дування, чи голод, чи нагота́, чи небезпека, чи меч?
36 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Saboda kai ne muke fuskantar mutuwa dukan yini; an ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.”
Як написано: „За Тебе нас цілий день умертвля́ють, нас уважають за овець, прирече́них на зако́лення“.
37 A’a, cikin dukan waɗannan abubuwa mun ma fi masu nasara ta wurin shi wanda ya ƙaunace mu.
Але в цьому всьому ми перемагаємо Тим, Хто нас полюбив.
38 Gama na tabbata cewa ko mutuwa ko rai, ko mala’iku ko aljanu, ko abubuwa na yanzu ko abubuwa masu zuwa nan gaba, ko ikoki,
Бо я пересві́дчився, що ні смерть, ні життя, ні анголи́, ні вла́ди, ні тепе́рішнє, ні майбу́тнє, ні сили,
39 ko tsayi ko zurfi, ko wani abu dabam cikin dukan halitta da zai iya raba mu da ƙaunar Allah wadda take cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.
ні вишина́, ні глибина́, ані інше яке створіння не зможе відлучити нас від любови Божої, яка в Христі Ісусі, Господі нашім!