< Romawa 7 >

1 Ba ku sani ba,’yan’uwa, ina magana ne fa da mutanen da suka san doka, cewa dokar tana da iko a kan mutum muddin yana a raye ne kawai.
Know ye not, brethren, ( for I speak to them that know the law, ) that the law hath dominion over a man as long as he liveth?
2 Misali, bisa ga doka mace mai aure tana daure ga mijinta muddin mijin yana da rai, amma in mijinta ya mutu, an sake ta ke nan daga dokar aure.
For the woman who hath an husband is bound by the law to her husband so long as he liveth; but if the husband is dead, she is loosed from the law of her husband.
3 Saboda haka fa, in ta auri wani yayinda mijinta yana raye, za a ce da ita mazinaciya. Amma in mijinta ya mutu, an sake ta ke nan daga wannan doka, ita kuwa ba mazinaciya ba ce, ko da yake ta auri wani.
So then if, while her husband liveth, she is married to another man, she shall be called an adulteress: but if her husband is dead, she is free from that law; so that she is no adulteress, though she be married to another man.
4 Saboda haka’yan’uwana, ku ma kun mutu ga dokar ta wurin jikin Kiristi, domin ku zama na wani, gare shi wanda aka tashe shi daga matattu, don mu ba da amfani ga Allah.
Therefore, my brethren, ye also are become dead to the law by the body of Christ; that ye should be married to another, even to him who is raised from the dead, that we should bring forth fruit to God.
5 Gama sa’ad da halin mutuntaka yake mulkinmu, sha’awace-sha’awacen zunubi waɗanda dokar ta zuga sun yi ta aiki a jikunanmu, don mu ba da amfani wa mutuwa.
For when we were in the flesh, the sinful passions, which were by the law, did work in our members to bring forth fruit to death.
6 Amma yanzu, ta wurin mutuwa ga abin da dā ya daure mu, an sake mu daga dokar saboda mu yi hidima a sabuwar hanyar Ruhu, ba a tsohuwar hanyar rubutaccen ƙa’ida ba.
But now we are delivered from the law, that being dead by which we were held; that we should serve in newness of spirit, and not in the oldness of the letter.
7 Me za mu ce ke nan? Dokar zunubi ce? Sam, ko kaɗan! Tabbatacce ai, da ban san mene ne zunubi ba in ba ta wurin doka ba. Gama da ban san mene ne ƙyashi yake ba tabbatacce in ba don doka ta ce, “Kada ka yi ƙyashi ba.”
What shall we say then? Is the law sin? By no means. Nay, I had not known sin, but by the law: for I had not known lust, except the law had said, Thou shalt not covet.
8 Amma zunubi, da ya sami dama ta wurin umarnin nan, ya haifar a cikina kowane halin ƙyashi iri-iri. Gama in babu doka, zunubi matacce ne.
But sin, taking occasion by the commandment, wrought in me all manner of lust. For apart from the law sin was dead.
9 Dā kam ina da rai sa’ad da ban san doka ba; amma da umarni ya zo, sai zunubi ya zaburo da rai na kuma mutu.
For I was alive apart from the law once: but when the commandment came, sin revived, and I died.
10 Na gane cewa wannan umarnin da aka nufa ya kawo rai, a gaskiya ya jawo mutuwa ce.
And the commandment, which was ordained to life, I found to be to death.
11 Gama zunubi, da ya sami dama ta wurin umarni, sai ya ruɗe ni, kuma ta wurin umarnin kuwa ya kashe ni.
For sin, taking occasion by the commandment, deceived me, and by it slew me.
12 Saboda haka fa, dokar tana da tsarki, umarnin kuma yana da tsarki, su duka suna da adalci da kuma kyau.
Therefore the law is holy, and the commandment holy, and just, and good.
13 Abin nan da yana mai kyau, zai kawo mini mutuwa? Ko kaɗan! Amma domin zunubi ya bayyana kansa a matsayin zunubi, sai ya haifar da mutuwa a cikina ta wurin abin da yake mai kyau, domin ta wurin umarnin nan zunubi ya fito da matuƙar muninsa.
Was then that which is good made death to me? By no means. But sin, that it might appear sin, working death in me by that which is good; that sin by the commandment might become exceeding sinful.
14 Mun san cewa doka aba ce ta ruhu; amma ni ba na ruhu ba ne, an sayar da ni a matsayin bawa ga zunubi.
For we know that the law is spiritual: but I am carnal, sold under sin.
15 Ban gane abin da nake yi ba. Don abin da nakan so yi, ba shi nakan yi ba, sai dai abin da nake ƙi, shi nake yi.
For that which I do I understand not: for what I would, that I do not; but what I hate, that I do.
16 In kuma na yi abin da ba na son yi, na yarda da cewa dokar aba ce mai kyau.
If then I do that which I would not, I consent to the law that it is good.
17 Kamar dai yadda yake, ba ni kaina nake yinsa ba, sai dai zunubin da yake zaune a cikina ne.
Now then it is no more I that do it, but sin that dwelleth in me.
18 Gama na san cewa babu wani abin kirkin da yake zaune a cikina, wato, a mutuntakata. Gama sha’awar yin abu mai kyau kam ina da ita, sai dai ikon yin ne fa babu.
For I know that in me (that is, in my flesh, ) dwelleth no good thing: for to will is present with me; but how to perform that which is good I find not.
19 Gama abin da nake yi ba shi ne abu mai kyau da nake so in yi ba; a’a, mugun da ba na so in yi, shi ne nake ci gaba da yi.
For the good that I would I do not: but the evil which I would not, that I do.
20 To, in na yi abin da ba na so in yi, ba ni ba ne nake yinsa, sai dai zunubin nan da yake zaune a cikina.
Now if I do that which I would not, it is no more I that do it, but sin that dwelleth in me.
21 Saboda haka na gane wannan ƙa’ida ce take aiki a cikina. Sa’ad da nake so in yi abu mai kyau, sai in ga cewa mugun nan ne nake yi.
I find then a law, that, when I would do good, evil is present with me.
22 Gama a ciki-cikina ina farin cikin da dokar Allah;
For I delight in the law of God after the inward man:
23 amma ina ganin wata doka tana aiki a gaɓoɓin jikina, tana yaƙi da dokar hankalina, tana kuma sa in zama ɗaurarren dokar zunubin da take aiki a gaɓoɓin jikina.
But I see another law in my members, warring against the law of my mind, and bringing me into captivity to the law of sin which is in my members.
24 Kaitona! Wane ne zai cece ni daga wannan jiki mai mutuwa?
O wretched man that I am! who shall deliver me from the body of this death?
25 Godiya ga Allah ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu! Saboda haka fa, ni kaina a cikin hankalina, ni bawa ne ga dokar Allah, amma a mutuntaka, ni bawa ne ga dokar zunubi.
I thank God through Jesus Christ our Lord. So then with the mind I myself serve the law of God; but with the flesh the law of sin.

< Romawa 7 >