< Romawa 7 >
1 Ba ku sani ba,’yan’uwa, ina magana ne fa da mutanen da suka san doka, cewa dokar tana da iko a kan mutum muddin yana a raye ne kawai.
Know ye not, brethren, (for I am speaking to those who are acquainted with the Law, ) that the Law hath dominion over a man only as long as he liveth?
2 Misali, bisa ga doka mace mai aure tana daure ga mijinta muddin mijin yana da rai, amma in mijinta ya mutu, an sake ta ke nan daga dokar aure.
For the married woman is bound by law to her husband while he liveth; but if the husband die, she is released from the law which bound her to him.
3 Saboda haka fa, in ta auri wani yayinda mijinta yana raye, za a ce da ita mazinaciya. Amma in mijinta ya mutu, an sake ta ke nan daga wannan doka, ita kuwa ba mazinaciya ba ce, ko da yake ta auri wani.
So then, if while her husband is living she connect herself with another man, she will be called an adulteress; but if her husband die, she is no longer bound by that law, so that she will not be an adulteress, though she connect herself with another man.
4 Saboda haka’yan’uwana, ku ma kun mutu ga dokar ta wurin jikin Kiristi, domin ku zama na wani, gare shi wanda aka tashe shi daga matattu, don mu ba da amfani ga Allah.
So then, my brethren, ye also were slain to the Law through the body of Christ, that ye might be connected with another, even with him who was raised from the dead, that we might bear fruit to God.
5 Gama sa’ad da halin mutuntaka yake mulkinmu, sha’awace-sha’awacen zunubi waɗanda dokar ta zuga sun yi ta aiki a jikunanmu, don mu ba da amfani wa mutuwa.
For when we were in the flesh, the affections of sins, which were through the Law, were working in our members to bear fruit unto death.
6 Amma yanzu, ta wurin mutuwa ga abin da dā ya daure mu, an sake mu daga dokar saboda mu yi hidima a sabuwar hanyar Ruhu, ba a tsohuwar hanyar rubutaccen ƙa’ida ba.
But now we are delivered from the Law, having died to that by which we were bound, that we might serve in the new life of the Spirit, and not in the old way of the letter.
7 Me za mu ce ke nan? Dokar zunubi ce? Sam, ko kaɗan! Tabbatacce ai, da ban san mene ne zunubi ba in ba ta wurin doka ba. Gama da ban san mene ne ƙyashi yake ba tabbatacce in ba don doka ta ce, “Kada ka yi ƙyashi ba.”
What then shall we say? Is the Law sin? God forbid! But I should not have known sin, except by the Law; for I should not have known sinful desire, unless the Law had said, “Thou shalt not covet.”
8 Amma zunubi, da ya sami dama ta wurin umarnin nan, ya haifar a cikina kowane halin ƙyashi iri-iri. Gama in babu doka, zunubi matacce ne.
But sin, seizing the opportunity, wrought in me by means of the commandment all manner of sinful desire; for without the Law sin is dead.
9 Dā kam ina da rai sa’ad da ban san doka ba; amma da umarni ya zo, sai zunubi ya zaburo da rai na kuma mutu.
And I, apart from the Law, was once alive; but when the commandment came, sin came to life again, and I died;
10 Na gane cewa wannan umarnin da aka nufa ya kawo rai, a gaskiya ya jawo mutuwa ce.
and the very commandment whose design was life, I found to issue in death.
11 Gama zunubi, da ya sami dama ta wurin umarni, sai ya ruɗe ni, kuma ta wurin umarnin kuwa ya kashe ni.
For sin, seizing the opportunity, deceived me through the commandment, and through it slew me.
12 Saboda haka fa, dokar tana da tsarki, umarnin kuma yana da tsarki, su duka suna da adalci da kuma kyau.
So that the Law is holy, and the commandment holy, and right, and good.
13 Abin nan da yana mai kyau, zai kawo mini mutuwa? Ko kaɗan! Amma domin zunubi ya bayyana kansa a matsayin zunubi, sai ya haifar da mutuwa a cikina ta wurin abin da yake mai kyau, domin ta wurin umarnin nan zunubi ya fito da matuƙar muninsa.
Did then that which is good become death to me? Far be it! but sin; that it might become manifest as sin, causing death to me by means of that which is good; that sin by means of the commandment might become exceedingly sinful.
14 Mun san cewa doka aba ce ta ruhu; amma ni ba na ruhu ba ne, an sayar da ni a matsayin bawa ga zunubi.
For we know that the Law is spiritual; but I am unspiritual, a slave sold to sin.
15 Ban gane abin da nake yi ba. Don abin da nakan so yi, ba shi nakan yi ba, sai dai abin da nake ƙi, shi nake yi.
For I know not what I do. For I do not what I would, but I do what I hate.
16 In kuma na yi abin da ba na son yi, na yarda da cewa dokar aba ce mai kyau.
But if I do what I would not, I assent to the Law that it is good.
17 Kamar dai yadda yake, ba ni kaina nake yinsa ba, sai dai zunubin da yake zaune a cikina ne.
Now, however, it is no longer I that do it, but sin that dwelleth in me.
18 Gama na san cewa babu wani abin kirkin da yake zaune a cikina, wato, a mutuntakata. Gama sha’awar yin abu mai kyau kam ina da ita, sai dai ikon yin ne fa babu.
For I know that there dwelleth not in me, that is, in my flesh, any good thing; for to desire is present with me, but not to perform that which is good.
19 Gama abin da nake yi ba shi ne abu mai kyau da nake so in yi ba; a’a, mugun da ba na so in yi, shi ne nake ci gaba da yi.
For the good that I would, I do not; but the evil which I would not, that I do.
20 To, in na yi abin da ba na so in yi, ba ni ba ne nake yinsa, sai dai zunubin nan da yake zaune a cikina.
But if I do what I would not, it is no more I that do it, but sin that dwelleth in me.
21 Saboda haka na gane wannan ƙa’ida ce take aiki a cikina. Sa’ad da nake so in yi abu mai kyau, sai in ga cewa mugun nan ne nake yi.
I find then that there is a law to me, that when I would do good, evil is present with me.
22 Gama a ciki-cikina ina farin cikin da dokar Allah;
For I delight in the Law of God, as to the inward man;
23 amma ina ganin wata doka tana aiki a gaɓoɓin jikina, tana yaƙi da dokar hankalina, tana kuma sa in zama ɗaurarren dokar zunubin da take aiki a gaɓoɓin jikina.
but I perceive another law in my members warring against the law of my mind, and bringing me into captivity to the law of sin which is in my members.
24 Kaitona! Wane ne zai cece ni daga wannan jiki mai mutuwa?
Wretched man that I am! Who will deliver me from the body of this death?
25 Godiya ga Allah ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu! Saboda haka fa, ni kaina a cikin hankalina, ni bawa ne ga dokar Allah, amma a mutuntaka, ni bawa ne ga dokar zunubi.
Thanks be to God, [[who hath delivered me]] through Jesus Christ our Lord. So then, I, the same person, with the mind serve the law of God, but with the flesh the law of sin.