< Romawa 6 >

1 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba da yin zunubi domin alheri yă haɓaka?
Ania ngarud ti ibagatayo? Agtultuloytayo kadi nga agbasol tapno umado ti parabur?
2 Sam, ko kaɗan! Mun mutu ga zunubi; ta yaya za mu ci gaba da rayuwa a cikinsa kuma?
Saan koma. Datayo a natay iti basol, kasano nga agbiagtayo pay latta iti daytoy?
3 Ko ba ku sani ba cewa dukanmu da aka yi wa baftisma a cikin Kiristi Yesu an yi mana baftismar ne zuwa cikin mutuwarsa?
Saanyo kadi nga ammo a ti kaadu iti nabautisaran kenni Cristo Jesus ket nabautisaran iti pannakatayna?
4 Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka tā da Kiristi daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa.
Kaduanatayo ngarud a naitabon babaen iti pannakabautisar iti ipapatay. Napasamak daytoy tapno kas iti pannakapagungar ni Cristo babaen iti dayag ti Ama, kasta met a magnatayo iti kinabaro ti biag.
5 In kuwa mun zama ɗaya tare da shi haka a cikin mutuwarsa, tabbatacce mu ma za mu zama ɗaya tare da shi cikin tashinsa daga matattu.
Ta no nakipagmaymaysatayo kenkuana iti ipapatayna, makipagmaymaysatayonto met iti panagungarna.
6 Gama mun san cewa an gicciye halayenmu na dā tare da shi domin a kawar da jikin nan mai zunubi don kada mu ƙara zama bayi ga zunubi
Ammotayo daytoy, a naikrus a kaduana ti daan a kinataotayo, tapno madadael ti bagi ti basol. Napasamak daytoy tapno saantayon nga agbalin a tagabu ti basol.
7 domin duk wanda ya mutu an’yantar da shi daga zunubi ke nan.
Naibilang a nalinteg ti tao a natay no maipapan iti basol.
8 To, in mun mutu tare da Kiristi, mun gaskata cewa za mu rayu tare da shi kuma.
Ngem no nataytayo a kadua ni Cristo, mamatitayo a makipagbiagtayo met kenkuana.
9 Gama mun san cewa da yake an tā da Kiristi daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba; mutuwa ba ta da sauran iko a kansa.
Ammotayo a napagungar ni Jesus manipud kadagiti natay, ken saanen a natay isuna. Saanen nga agturay ti patay kenkuana ni kaanoman.
10 Mutuwar da ya yi, ya mutu ne sau ɗaya tak, saboda yă shafe zunubi, amma rayuwar da yake yi, yana yi ne cikin tarayya da Allah.
Ta maipapan iti ipapatay a nakatayanna iti basol, natay isuna a naminpinsan para iti amin. Nupay kasta, ti biag a pagbibiaganna, pagbibiaganna daytoy a para iti Dios.
11 Haka ku ma, ku ɗauke kanku matattu ne ga ikon zunubi amma rayayyu cikin tarayya da Allah cikin Kiristi Yesu.
Iti isu met laeng a wagas, masapul met nga ibilangyo dagiti bagbagiyo a natay iti basol, ngem sibibiag iti Dios kenni Cristo Jesus.
12 Saboda haka kada ku bar zunubi yă mallaki jikin nan naku mai mutuwa yă sa ku zama masu biyayya ga mugayen sha’awace-sha’awacensa.
Ngarud, saanyo nga itulok nga agturay ti basol iti nainlasagan a bagiyo tapno pagtulnoganyo ti gartemna.
13 Kada ku miƙa gaɓoɓin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin mugunta, sai dai ku miƙa kanku ga Allah, a matsayin waɗanda aka fitar da su daga mutuwa zuwa rai; ku kuma miƙa gaɓoɓin jikinku gare shi a matsayin kayan aikin adalci.
Saanyo nga idatag dagiti paset ti bagiyo iti basol a maaramat iti kinaawan linteg, ngem idatagyo dagiti bagbagiyo iti Dios, kas sibibiag manipud iti patay. Ket idatagyo dagiti paset ti bagiyo a maaramat iti kinalinteg a maipaay iti Dios.
14 Gama zunubi ba zai zama maigidanku ba, domin ba kwa ƙarƙashin doka, sai dai ƙarƙashin alheri.
Saanyo nga ipalubos nga agturay ti basol kadakayo. Ta awankayon iti linteg no di ket iti parabur.
15 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba yin zunubi domin ba ma ƙarƙashin doka sai dai ƙarƙashin alheri? Sam, ko kaɗan!
Ania ngaruden? Agbasoltayo kadi gapu ta awantayo iti panangituray ti linteg, ngem iti panangituray ti parabur? Saan koma.
16 Ba ku sani ba cewa sa’ad da kuka miƙa kanku ga wani don ku yi masa biyayya a matsayin bayi, ko ku bayi ne ga zunubi, wanda yake kai ga mutuwa, ko kuwa ga biyayya, wadda take kai ga adalci, ashe, ba kun zama bayi ga wannan da kuke yi wa biyayya ba ke nan?
Saanyo kadi nga ammo a ti pangidataganyo iti bagiyo kas adipen, isu dayta ti nagbalinanyo nga adipen, ti rumbeng a pagtulnoganyo? Pudno daytoy nga adipennakayo man ti basol a mangiturong kadakayo iti patay wenno adipennakayo ti panagtulnog a mangiturong kadakayo iti kinalinteg.
17 Amma godiya ga Allah don ko da yake a dā ku bayi ne ga ikon zunubi, da dukan zuciyarku kun yi biyayya ga irin koyarwar da aka danƙa muku.
Ngem agyamanak iti Dios! Ta nagbalinkayo nga adipen ti basol, ngem nagtulnogkayo a sipupuso iti kita ti sursuro a naited kadakayo.
18 An’yanta ku daga zunubi, kun kuma zama bayi ga aikin adalci.
Nawayawayaankayo manipud iti basol, ken napagbalinkayon nga adipen ti kinalinteg.
19 Ina magana ne kamar mutane saboda kun raunana a jikinku. Kamar yadda kuka saba miƙa gaɓoɓin jikinku a bautar abubuwan ƙazanta da mugun aiki a kan mugun aiki, saboda haka yanzu sai ku miƙa su bayi ga aikin adalci mai kai ga zaman tsarki.
Agsasaoak a kas tao gapu iti kinakapuy ti lasagyo. Ta idi indatagyo dagiti paset ti bagiyo kas tagabu iti kinarugit ken iti dakes, iti isu met laeng a wagas ita, idatagyo ti bagiyo a kas tagabu ti kinalinteg para iti pannakapasanto.
20 Sa’ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci.
Ta idi adipennakayo ti basol, nawayakayo manipud iti kinalinteg.
21 Wace riba ce kuka samu a lokacin, daga abubuwan nan da yanzu suka zama muku abin kunya? Ƙarshen irin abubuwan nan dai, mutuwa ne!
Iti dayta a tiempo, ania a bunga ti naadda kadakayo manipud kadagiti banbanag nga ibainyo ita? Ta patay ti pagbanagan dagitoy a banbanag.
22 Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios g166)
Ngem ita ta nawayawayaankayon manipud iti basol ken nagbalinkayo a tagabu ti Dios, adda kadakayo ti bungayo para iti pannakapasanto. Agnanayon a biag ti pagbanaganna. (aiōnios g166)
23 Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios g166)
Ta patay ti bayad ti basol, ngem ti awan bayadna a sagut ti Dios ket agnanayon a biag kenni Cristo Jesus nga Apotayo. (aiōnios g166)

< Romawa 6 >