< Romawa 6 >
1 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba da yin zunubi domin alheri yă haɓaka?
What shall we say then? Shall we continue in sin, that grace may abound?
2 Sam, ko kaɗan! Mun mutu ga zunubi; ta yaya za mu ci gaba da rayuwa a cikinsa kuma?
God forbid! how shall we, who are dead to sin, live any longer therein?
3 Ko ba ku sani ba cewa dukanmu da aka yi wa baftisma a cikin Kiristi Yesu an yi mana baftismar ne zuwa cikin mutuwarsa?
Know ye not, that as many of us as were baptized into Jesus Christ, were baptized into his death?
4 Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka tā da Kiristi daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa.
Therefore we are buried with Him by baptism into death: that as Christ was raised from the dead by the glory of the Father, so we also should walk in newness of life:
5 In kuwa mun zama ɗaya tare da shi haka a cikin mutuwarsa, tabbatacce mu ma za mu zama ɗaya tare da shi cikin tashinsa daga matattu.
for if we have been planted together in the resemblance of his death, so shall we be also of his resurrection.
6 Gama mun san cewa an gicciye halayenmu na dā tare da shi domin a kawar da jikin nan mai zunubi don kada mu ƙara zama bayi ga zunubi
Knowing this, that our old man is crucified with Him, that the body of sin might be destroyed, that we might no longer be inslaved to sin:
7 domin duk wanda ya mutu an’yantar da shi daga zunubi ke nan.
for he that is thus dead with Christ, is delivered from sin.
8 To, in mun mutu tare da Kiristi, mun gaskata cewa za mu rayu tare da shi kuma.
Now if we be dead with Christ, we believe that we shall also live with Him:
9 Gama mun san cewa da yake an tā da Kiristi daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba; mutuwa ba ta da sauran iko a kansa.
knowing that Christ being raised from the dead dieth no more; death hath no more power over Him: for as He died, He died once for all on account of sin;
10 Mutuwar da ya yi, ya mutu ne sau ɗaya tak, saboda yă shafe zunubi, amma rayuwar da yake yi, yana yi ne cikin tarayya da Allah.
but as He liveth, He liveth unto God.
11 Haka ku ma, ku ɗauke kanku matattu ne ga ikon zunubi amma rayayyu cikin tarayya da Allah cikin Kiristi Yesu.
So also do ye reckon yourselves to be dead indeed unto sin, but alive unto God in Christ Jesus our Lord.
12 Saboda haka kada ku bar zunubi yă mallaki jikin nan naku mai mutuwa yă sa ku zama masu biyayya ga mugayen sha’awace-sha’awacensa.
Let not sin therefore reign in your mortal body, to obey it in the lusts thereof.
13 Kada ku miƙa gaɓoɓin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin mugunta, sai dai ku miƙa kanku ga Allah, a matsayin waɗanda aka fitar da su daga mutuwa zuwa rai; ku kuma miƙa gaɓoɓin jikinku gare shi a matsayin kayan aikin adalci.
Neither yield your bodies as instruments of unrighteousness unto sin: but present yourselves to God as alive from the dead, and your bodies as instruments of righteousness to God.
14 Gama zunubi ba zai zama maigidanku ba, domin ba kwa ƙarƙashin doka, sai dai ƙarƙashin alheri.
For sin shall have no power over you, inasmuch as ye are not under the law, but under grace.
15 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba yin zunubi domin ba ma ƙarƙashin doka sai dai ƙarƙashin alheri? Sam, ko kaɗan!
What then? shall we sin, because we are not under the law, but under grace?
16 Ba ku sani ba cewa sa’ad da kuka miƙa kanku ga wani don ku yi masa biyayya a matsayin bayi, ko ku bayi ne ga zunubi, wanda yake kai ga mutuwa, ko kuwa ga biyayya, wadda take kai ga adalci, ashe, ba kun zama bayi ga wannan da kuke yi wa biyayya ba ke nan?
God forbid! Know ye not, that to whom ye present yourselves servants to obedience, his servants ye are whom ye obey? either of sin unto death, or of obedience unto righteousness?
17 Amma godiya ga Allah don ko da yake a dā ku bayi ne ga ikon zunubi, da dukan zuciyarku kun yi biyayya ga irin koyarwar da aka danƙa muku.
But thanks be to God, that ye who were servants of sin, have obeyed from the heart that form of doctrine which was delivered to you:
18 An’yanta ku daga zunubi, kun kuma zama bayi ga aikin adalci.
and being set free from sin, ye are become the servants of righteousness.
19 Ina magana ne kamar mutane saboda kun raunana a jikinku. Kamar yadda kuka saba miƙa gaɓoɓin jikinku a bautar abubuwan ƙazanta da mugun aiki a kan mugun aiki, saboda haka yanzu sai ku miƙa su bayi ga aikin adalci mai kai ga zaman tsarki.
I speak after the manner of men, because of the infirmity of your flesh: as ye have yielded your bodies servants to impurity and iniquity to work iniquity; so now present your bodies servants to righteousness, unto holiness.
20 Sa’ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci.
For when ye were servants of sin, ye were free from righteousness.
21 Wace riba ce kuka samu a lokacin, daga abubuwan nan da yanzu suka zama muku abin kunya? Ƙarshen irin abubuwan nan dai, mutuwa ne!
What fruit therefore had ye then in the things, which ye are now ashamed of? for the end of those things is death.
22 Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios )
But now being set free from sin, and become servants to God, ye have your fruit unto holiness, and the end everlasting life. (aiōnios )
23 Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios )
For the wages of sin is death: but the gift of God is eternal life through Jesus Christ our Lord. (aiōnios )