< Romawa 6 >

1 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba da yin zunubi domin alheri yă haɓaka?
To what conclusion, then, shall we come? Are we to persist in sinning in order that the grace extended to us may be the greater?
2 Sam, ko kaɗan! Mun mutu ga zunubi; ta yaya za mu ci gaba da rayuwa a cikinsa kuma?
No, indeed; how shall we who have died to sin, live in it any longer?
3 Ko ba ku sani ba cewa dukanmu da aka yi wa baftisma a cikin Kiristi Yesu an yi mana baftismar ne zuwa cikin mutuwarsa?
And do you not know that all of us who have been baptized into Christ Jesus were baptized into His death?
4 Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka tā da Kiristi daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa.
Well, then, we by our baptism were buried with Him in death, in order that, just as Christ was raised from among the dead by the Father's glorious power, we also should live an entirely new life.
5 In kuwa mun zama ɗaya tare da shi haka a cikin mutuwarsa, tabbatacce mu ma za mu zama ɗaya tare da shi cikin tashinsa daga matattu.
For since we have become one with Him by sharing in His death, we shall also be one with Him by sharing in His resurrection.
6 Gama mun san cewa an gicciye halayenmu na dā tare da shi domin a kawar da jikin nan mai zunubi don kada mu ƙara zama bayi ga zunubi
This we know--that our old self was nailed to the cross with Him, in order that our sinful nature might be deprived of its power, so that we should no longer be the slaves of sin;
7 domin duk wanda ya mutu an’yantar da shi daga zunubi ke nan.
for he who has paid the penalty of death stands absolved from his sin.
8 To, in mun mutu tare da Kiristi, mun gaskata cewa za mu rayu tare da shi kuma.
But, seeing that we have died with Christ, we believe that we shall also live with Him;
9 Gama mun san cewa da yake an tā da Kiristi daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba; mutuwa ba ta da sauran iko a kansa.
because we know that Christ, having come back to life, is no longer liable to die.
10 Mutuwar da ya yi, ya mutu ne sau ɗaya tak, saboda yă shafe zunubi, amma rayuwar da yake yi, yana yi ne cikin tarayya da Allah.
Death has no longer any power over Him. For by the death which He died He became, once for all, dead in relation to sin; but by the life which He now lives He is alive in relation to God.
11 Haka ku ma, ku ɗauke kanku matattu ne ga ikon zunubi amma rayayyu cikin tarayya da Allah cikin Kiristi Yesu.
In the same way you also must regard yourselves as dead in relation to sin, but as alive in relation to God, because you are in Christ Jesus.
12 Saboda haka kada ku bar zunubi yă mallaki jikin nan naku mai mutuwa yă sa ku zama masu biyayya ga mugayen sha’awace-sha’awacensa.
Let not Sin therefore reign as king in your mortal bodies, causing you to be in subjection to their cravings;
13 Kada ku miƙa gaɓoɓin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin mugunta, sai dai ku miƙa kanku ga Allah, a matsayin waɗanda aka fitar da su daga mutuwa zuwa rai; ku kuma miƙa gaɓoɓin jikinku gare shi a matsayin kayan aikin adalci.
and no longer lend your faculties as unrighteous weapons for Sin to use. On the contrary surrender your very selves to God as living men who have risen from the dead, and surrender your several faculties to God, to be used as weapons to maintain the right.
14 Gama zunubi ba zai zama maigidanku ba, domin ba kwa ƙarƙashin doka, sai dai ƙarƙashin alheri.
For Sin shall not be lord over you, since you are subjects not of Law, but of grace.
15 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba yin zunubi domin ba ma ƙarƙashin doka sai dai ƙarƙashin alheri? Sam, ko kaɗan!
Are we therefore to sin because we are no longer under the authority of Law, but under grace? No, indeed!
16 Ba ku sani ba cewa sa’ad da kuka miƙa kanku ga wani don ku yi masa biyayya a matsayin bayi, ko ku bayi ne ga zunubi, wanda yake kai ga mutuwa, ko kuwa ga biyayya, wadda take kai ga adalci, ashe, ba kun zama bayi ga wannan da kuke yi wa biyayya ba ke nan?
Do you not know that if you surrender yourselves as bondservants to obey any one, you become the bondservants of him whom you obey, whether the bondservants of Sin (with death as the result) or of Duty (resulting in righteousness)?
17 Amma godiya ga Allah don ko da yake a dā ku bayi ne ga ikon zunubi, da dukan zuciyarku kun yi biyayya ga irin koyarwar da aka danƙa muku.
But thanks be to God that though you were once in thraldom to Sin, you have now yielded a hearty obedience to that system of truth in which you have been instructed.
18 An’yanta ku daga zunubi, kun kuma zama bayi ga aikin adalci.
You were set free from the tyranny of Sin, and became the bondservants of Righteousness--
19 Ina magana ne kamar mutane saboda kun raunana a jikinku. Kamar yadda kuka saba miƙa gaɓoɓin jikinku a bautar abubuwan ƙazanta da mugun aiki a kan mugun aiki, saboda haka yanzu sai ku miƙa su bayi ga aikin adalci mai kai ga zaman tsarki.
your human infirmity leads me to employ these familiar figures--and just as you once surrendered your faculties into bondage to Impurity and ever-increasing disregard of Law, so you must now surrender them into bondage to Righteousness ever advancing towards perfect holiness.
20 Sa’ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci.
For when you were the bondservants of sin, you were under no sort of subjection to Righteousness.
21 Wace riba ce kuka samu a lokacin, daga abubuwan nan da yanzu suka zama muku abin kunya? Ƙarshen irin abubuwan nan dai, mutuwa ne!
At that time, then, what benefit did you get from conduct which you now regard with shame? Why, such things finally result in death.
22 Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios g166)
But now that you have been set free from the tyranny of Sin, and have become the bondservants of God, you have your reward in being made holy, and you have the Life of the Ages as the final result. (aiōnios g166)
23 Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios g166)
For the wages paid by Sin are death; but God's free gift is the Life of the Ages bestowed upon us in Christ Jesus our Lord. (aiōnios g166)

< Romawa 6 >