< Romawa 6 >
1 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba da yin zunubi domin alheri yă haɓaka?
What shall we say then? Shall we continue in sin, that grace may abound?
2 Sam, ko kaɗan! Mun mutu ga zunubi; ta yaya za mu ci gaba da rayuwa a cikinsa kuma?
God forbid. We who died to sin, how shall we any longer live therein?
3 Ko ba ku sani ba cewa dukanmu da aka yi wa baftisma a cikin Kiristi Yesu an yi mana baftismar ne zuwa cikin mutuwarsa?
Or are ye ignorant that all we who were baptized into Christ Jesus were baptized into his death?
4 Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka tā da Kiristi daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa.
We were buried therefore with him through baptism into death: that like as Christ was raised from the dead through the glory of the Father, so we also might walk in newness of life.
5 In kuwa mun zama ɗaya tare da shi haka a cikin mutuwarsa, tabbatacce mu ma za mu zama ɗaya tare da shi cikin tashinsa daga matattu.
For if we have become united with [him] by the likeness of his death, we shall be also [by the likeness] of his resurrection;
6 Gama mun san cewa an gicciye halayenmu na dā tare da shi domin a kawar da jikin nan mai zunubi don kada mu ƙara zama bayi ga zunubi
knowing this, that our old man was crucified with [him], that the body of sin might be done away, that so we should no longer be in bondage to sin;
7 domin duk wanda ya mutu an’yantar da shi daga zunubi ke nan.
for he that hath died is justified from sin.
8 To, in mun mutu tare da Kiristi, mun gaskata cewa za mu rayu tare da shi kuma.
But if we died with Christ, we believe that we shall also live with him;
9 Gama mun san cewa da yake an tā da Kiristi daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba; mutuwa ba ta da sauran iko a kansa.
knowing that Christ being raised from the dead dieth no more; death no more hath dominion over him.
10 Mutuwar da ya yi, ya mutu ne sau ɗaya tak, saboda yă shafe zunubi, amma rayuwar da yake yi, yana yi ne cikin tarayya da Allah.
For the death that he died, he died unto sin once: but the life that he liveth, he liveth unto God.
11 Haka ku ma, ku ɗauke kanku matattu ne ga ikon zunubi amma rayayyu cikin tarayya da Allah cikin Kiristi Yesu.
Even so reckon ye also yourselves to be dead unto sin, but alive unto God in Christ Jesus.
12 Saboda haka kada ku bar zunubi yă mallaki jikin nan naku mai mutuwa yă sa ku zama masu biyayya ga mugayen sha’awace-sha’awacensa.
Let not sin therefore reign in your mortal body, that ye should obey the lusts thereof:
13 Kada ku miƙa gaɓoɓin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin mugunta, sai dai ku miƙa kanku ga Allah, a matsayin waɗanda aka fitar da su daga mutuwa zuwa rai; ku kuma miƙa gaɓoɓin jikinku gare shi a matsayin kayan aikin adalci.
neither present your members unto sin [as] instruments of unrighteousness; but present yourselves unto God, as alive from the dead, and your members [as] instruments of righteousness unto God.
14 Gama zunubi ba zai zama maigidanku ba, domin ba kwa ƙarƙashin doka, sai dai ƙarƙashin alheri.
For sin shall not have dominion over you: for ye are not under law, but under grace.
15 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba yin zunubi domin ba ma ƙarƙashin doka sai dai ƙarƙashin alheri? Sam, ko kaɗan!
What then? shall we sin, because we are not under law, but under grace? God forbid.
16 Ba ku sani ba cewa sa’ad da kuka miƙa kanku ga wani don ku yi masa biyayya a matsayin bayi, ko ku bayi ne ga zunubi, wanda yake kai ga mutuwa, ko kuwa ga biyayya, wadda take kai ga adalci, ashe, ba kun zama bayi ga wannan da kuke yi wa biyayya ba ke nan?
Know ye not, that to whom ye present yourselves [as] servants unto obedience, his servants ye are whom ye obey; whether of sin unto death, or of obedience unto righteousness?
17 Amma godiya ga Allah don ko da yake a dā ku bayi ne ga ikon zunubi, da dukan zuciyarku kun yi biyayya ga irin koyarwar da aka danƙa muku.
But thanks be to God, that, whereas ye were servants of sin, ye became obedient from the heart to that form of teaching whereunto ye were delivered;
18 An’yanta ku daga zunubi, kun kuma zama bayi ga aikin adalci.
and being made free from sin, ye became servants of righteousness.
19 Ina magana ne kamar mutane saboda kun raunana a jikinku. Kamar yadda kuka saba miƙa gaɓoɓin jikinku a bautar abubuwan ƙazanta da mugun aiki a kan mugun aiki, saboda haka yanzu sai ku miƙa su bayi ga aikin adalci mai kai ga zaman tsarki.
I speak after the manner of men because of the infirmity of your flesh: for as ye presented your members [as] servants to uncleanness and to iniquity unto iniquity, even so now present your members [as] servants to righteousness unto sanctification.
20 Sa’ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci.
For when ye were servants of sin, ye were free in regard of righteousness.
21 Wace riba ce kuka samu a lokacin, daga abubuwan nan da yanzu suka zama muku abin kunya? Ƙarshen irin abubuwan nan dai, mutuwa ne!
What fruit then had ye at that time in the things whereof ye are now ashamed? for the end of those things is death.
22 Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios )
But now being made free from sin, and become servants to God, ye have your fruit unto sanctification, and the end eternal life. (aiōnios )
23 Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios )
For the wages of sin is death; but the free gift of God is eternal life in Christ Jesus our Lord. (aiōnios )