< Romawa 5 >

1 Saboda haka, da yake an same mu marasa laifi ta wurin bangaskiya, muna da salama tare da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi,
Då vi nu hava blivit rättfärdiggjorda av tro, hava vi frid med Gud genom vår Herre Jesus Kristus
2 ta wurinsa ne muka sami shiga wannan alherin da muke tsaye yanzu, ta wurin bangaskiya. Muna kuma farin ciki a begen ɗaukakar Allah.
-- genom vilken vi ock hava fått tillträde till den nåd vari vi nu stå -- och vi berömma oss i hoppet om Guds härlighet.
3 Ba haka kawai ba, amma muna kuma da farin ciki cikin shan wuyanmu, gama mun san cewa shan wuyan nan takan haifi jimiri;
Och icke det allenast, vi till och med berömma oss av våra lidanden, eftersom vi veta att lidandet verkar ståndaktighet,
4 jimiri kuma yakan kawo hali mai kyau; hali mai kyau kuma yakan sa bege.
och ståndaktigheten beprövad fasthet, och fastheten hopp,
5 Bege kuwa ba ya ba mu kunya, domin Allah ya zuba ƙaunarsa a zukatanmu ta wurin Ruhu Mai Tsarkin da ya ba mu.
och hoppet låter oss icke komma på skam; ty Guds kärlek är utgjuten i våra hjärtan genom den helige Ande, vilken har blivit oss given.
6 Kun ga, a daidai lokaci, yayinda muke marasa ƙarfi, Kiristi ya mutu saboda waɗanda ba su san Allah ba.
Ty medan vi ännu voro svaga, led Kristus, när tiden var inne, döden för oss ogudaktiga.
7 Da ƙyar wani yă mutu saboda mai adalci, ko da yake saboda mutumin kirki wani zai iya ƙarfin hali yă mutu.
Näppeligen vill ju eljest någon dö ens för en rättfärdig man -- om nu ock till äventyrs någon kan hava mod att dö för den som har gjort honom gott --
8 Amma Allah ya nuna mana ƙaunarsa a wannan. Tun muna masu zunubi tukuna, Kiristi ya mutu dominmu.
men Gud bevisar sin kärlek till oss däri att Kristus dog för oss, medan vi ännu voro syndare.
9 Da yake yanzu mun sami zama marasa laifi ta wurin jininsa, ashe kuwa za a cece mu daga fushin Allah ta wurinsa!
Så mycket mer skola vi därför, sedan vi nu hava blivit rättfärdiggjorda i och genom hans blod, också genom honom bliva frälsta undan vredesdomen.
10 Gama in kuwa, sa’ad da muke abokan gāban Allah, aka sulhunta mu da shi ta wurin mutuwar Ɗansa, ashe, da yake an sulhunta mu, za mu sami ceto ta wurin ransa!
Ty om vi, medan vi voro Guds ovänner, blevo försonade med honom genom hans Sons död, så skola vi, sedan vi hava blivit försonade, ännu mycket mer bliva frälsta i och genom hans liv.
11 Ba ma haka yake kawai ba, har muna farin ciki da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa yanzu muka sami sulhu.
Och icke det allenast; vi berömma oss ock av Gud genom vår Herre Jesus Kristus, genom vilken vi nu hava undfått försoningen.
12 Saboda haka, kamar yadda zunubi ya shigo duniya ta wurin mutum ɗaya, mutuwa kuma ta wurin zunubi, ta haka kuwa mutuwa ta shafi dukan mutane, domin dukan mutane sun yi zunubi.
Därför är det så: Genom en enda människa har synden kommit in i världen och genom synden döden; och så har döden kommit över alla människor, eftersom de alla hava syndat.
13 Gama kafin a ba da doka, zunubi yana nan a duniya. Amma ba a lissafin zunubi inda babu doka.
Ty synd fanns i världen redan innan lagen fanns. Men synd tillräknas icke där ingen lag finnes;
14 Duk da haka, mutuwa ta yi mulki tun Adamu har yă zuwa Musa, ta yi mulki har ma a kan waɗanda ba su yi zunubi ta wurin taka umarni kamar yadda Adamu ya yi ba. A wata hanya dai Adamu shi ne kwatancin wani mutumin nan mai zuwa.
och dock har under tiden från Adam till Moses döden haft väldet också över dem som icke hade syndat genom en överträdelse, i likhet med vad Adam gjorde, han som är en förebild till den som skulle komma.
15 Amma kyautan nan dabam take da laifin nan. Gama in mutane da yawa sun mutu saboda laifin mutum ɗayan nan, to, ai, alherin Allah da kuma kyautan nan mai zuwa ta wurin alherin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi, ya shafi mutane da yawa!
Likväl är det icke så med nådegåvan, som det var med syndafallet. Ty om genom en endas fall de många hava blivit döden underlagda, så har ännu mycket mer Guds nåd och gåvan i och genom nåd -- vilken, också den, är kommen genom en enda människa, Jesus Kristus -- blivit på ett överflödande sätt de många beskärd.
16 Kyautar Allah kuwa ba kamar sakamakon da ya bi zunubin mutum gudan nan ba ne, Hukuncin ya bi zunubin mutum gudan nan, ya kuma kawo hallaka, amma kyautar ta bi laifofin masu yawa ta kuma sa Allah ya gan mu a matsayin marasa laifi.
Och med gåvan är det icke såsom det var med det som kom genom denne ene som syndade: domen kom genom en enda, och ledde till en fördömelsedom, men nådegåvan kom i följd av mångas fall, och ledde till en rättfärdiggörelsedom.
17 Gama in, ta wurin laifin mutum ɗaya, mutuwa ta yi mulki ta wurin mutum ɗayan nan, ashe, waɗanda suka sami kyautar alherin Allah a yalwace da kuma kyautar adalci za su yi mulki a wannan rayuwa ta wurin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi.
Och om döden på grund av en endas fall kom till konungavälde genom denne ene, så skola ännu mycket mer de som undfå den överflödande nåden och rättfärdighetsgåvan få konungsligt välde i liv, också det genom en enda, Jesus Kristus. --
18 Saboda haka, kamar yadda sakamakon laifin mutum guda ya jawo hallaka ga dukan mutane, haka ma sakamakon aikin adalci guda ya sa Allah ya same mu marasa laifi, wannan kuwa kawo rai ga dukan mutane.
Alltså, likasom det, som kom genom en endas fall, för alla människor ledde till en fördömelsedom, så leder det, som kom genom rättfärdiggörelsedomen förmedelst en enda, för alla människor till en rättfärdiggörelse som medför liv.
19 Gama kamar yadda ta wurin rashin biyayyar mutum guda, mutane masu yawa suka zama masu zunubi, haka kuma ta wurin biyayyar mutum guda, mutane da yawa za su zama masu adalci.
Ty såsom genom en enda människas olydnad de många fingo stå såsom syndare, så skola ock genom en endas lydnad de många stå såsom rättfärdiga.
20 An ba da dokar don mu ga yadda laifi yake da girma. Amma da zunubi ya ƙaru, sai alheri ya ƙaru sosai,
Men lagen har därjämte kommit in, för att fallet skulle bliva så mycket större; dock, där synden blev större, där överflödade nåden mycket mer.
21 domin, kamar yadda zunubi ya yi mulki cikin mutuwa, haka ma alheri yă yi mulki ta wurin adalci yă kuwa kawo rai madawwami ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu. (aiōnios g166)
Ty såsom synden hade utövat sitt välde i och genom döden, så skulle nu ock nåden genom rättfärdighet utöva sitt välde till evigt liv, och det genom Jesus Kristus, vår Herre. (aiōnios g166)

< Romawa 5 >