< Romawa 5 >

1 Saboda haka, da yake an same mu marasa laifi ta wurin bangaskiya, muna da salama tare da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi,
Opravičivši se torej z vero, imamo mir z Bogom po Gospodu našem Jezusu Kristusu,
2 ta wurinsa ne muka sami shiga wannan alherin da muke tsaye yanzu, ta wurin bangaskiya. Muna kuma farin ciki a begen ɗaukakar Allah.
Po kterem smo tudi pristop dobili z vero v to milost, v kterej stojimo in hvalimo se z upom slave Božje.
3 Ba haka kawai ba, amma muna kuma da farin ciki cikin shan wuyanmu, gama mun san cewa shan wuyan nan takan haifi jimiri;
Pa ne samo to, nego se tudi hvalimo v stiskah vedoč, da stiska potrpljivost dela,
4 jimiri kuma yakan kawo hali mai kyau; hali mai kyau kuma yakan sa bege.
A potrpljivost izkušenost, izkušenost pa up,
5 Bege kuwa ba ya ba mu kunya, domin Allah ya zuba ƙaunarsa a zukatanmu ta wurin Ruhu Mai Tsarkin da ya ba mu.
A up ne osramočuje, ker je ljubezen Božja izlita v srcih naših po Duhu svetem danem nam.
6 Kun ga, a daidai lokaci, yayinda muke marasa ƙarfi, Kiristi ya mutu saboda waɗanda ba su san Allah ba.
Kajti Kristus je, ko smo mi še slabi bili, svoj čas za nepobožne umrl,
7 Da ƙyar wani yă mutu saboda mai adalci, ko da yake saboda mutumin kirki wani zai iya ƙarfin hali yă mutu.
Ker bo težko kdo za pravičnega umiral, za dobrega lahko da se kdo drzne umreti.
8 Amma Allah ya nuna mana ƙaunarsa a wannan. Tun muna masu zunubi tukuna, Kiristi ya mutu dominmu.
Pokazuje pa Bog svojo ljubezen do nas, da je, ko smo mi še grešniki bili, Kristus za nas umrl.
9 Da yake yanzu mun sami zama marasa laifi ta wurin jininsa, ashe kuwa za a cece mu daga fushin Allah ta wurinsa!
Mnogo bolje se bomo torej, opravičivši se sedaj v krvi njegovej, po njem jeze rešili.
10 Gama in kuwa, sa’ad da muke abokan gāban Allah, aka sulhunta mu da shi ta wurin mutuwar Ɗansa, ashe, da yake an sulhunta mu, za mu sami ceto ta wurin ransa!
Kajti če smo se spravili z Bogom s smrtjo njegovega sina, dokler smo sovražniki bili, s tem bolje se bomo zveličali spravivši se v njegovem življenji.
11 Ba ma haka yake kawai ba, har muna farin ciki da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa yanzu muka sami sulhu.
Pa ne samo to, nego se tudi hvalimo z Bogom po Gospodu svojem Jezusu Kristusu, po kterem smo sedaj spravo dobili.
12 Saboda haka, kamar yadda zunubi ya shigo duniya ta wurin mutum ɗaya, mutuwa kuma ta wurin zunubi, ta haka kuwa mutuwa ta shafi dukan mutane, domin dukan mutane sun yi zunubi.
Za to kakor je po enem človeku greh na svet prišel in po grehu smrt, in tako je na vse ljudî smrt prišla, v komer so vsi pregrešili.
13 Gama kafin a ba da doka, zunubi yana nan a duniya. Amma ba a lissafin zunubi inda babu doka.
Kajti greh je bil noter do postave na svetu, ali se greh ne računi, dokler ni postave.
14 Duk da haka, mutuwa ta yi mulki tun Adamu har yă zuwa Musa, ta yi mulki har ma a kan waɗanda ba su yi zunubi ta wurin taka umarni kamar yadda Adamu ya yi ba. A wata hanya dai Adamu shi ne kwatancin wani mutumin nan mai zuwa.
Nego zakraljevala je smrt od Adama do Mojzesa tudi nad temi, kteri niso pregrešili na spodobo Adamovega prestopa, kteri je podoba tega, kteri je imel priti.
15 Amma kyautan nan dabam take da laifin nan. Gama in mutane da yawa sun mutu saboda laifin mutum ɗayan nan, to, ai, alherin Allah da kuma kyautan nan mai zuwa ta wurin alherin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi, ya shafi mutane da yawa!
Ali ni kakor pregreha tako tudi dar, kajti če so po pregrehi enega mnogi pomrli, za mnogo boljo se jo milost Božja in dar v milosti enega človeka Jezusa Kristusa na mnoge poobilšal.
16 Kyautar Allah kuwa ba kamar sakamakon da ya bi zunubin mutum gudan nan ba ne, Hukuncin ya bi zunubin mutum gudan nan, ya kuma kawo hallaka, amma kyautar ta bi laifofin masu yawa ta kuma sa Allah ya gan mu a matsayin marasa laifi.
In dar ni kakor greh enega, ker obsojenje je bilo iz ene pregrehe na pogubo, a dar iz mnogih pregreh na opravičenje.
17 Gama in, ta wurin laifin mutum ɗaya, mutuwa ta yi mulki ta wurin mutum ɗayan nan, ashe, waɗanda suka sami kyautar alherin Allah a yalwace da kuma kyautar adalci za su yi mulki a wannan rayuwa ta wurin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi.
Kajti če je za pregreho enega smrt zakraljevala po tem enem, za mnogo bolje bodo tisti, kteri prejemajo obilnost milosti in darú pravice, v življenji kraljevali po enem Jezusu Kristusu.
18 Saboda haka, kamar yadda sakamakon laifin mutum guda ya jawo hallaka ga dukan mutane, haka ma sakamakon aikin adalci guda ya sa Allah ya same mu marasa laifi, wannan kuwa kawo rai ga dukan mutane.
Kakor je torej po pregrehi enega prišlo obsojenje na vse ljudi, tako je tudi po pravičnosti enega prišlo na vse ljudi opravičenje življenja.
19 Gama kamar yadda ta wurin rashin biyayyar mutum guda, mutane masu yawa suka zama masu zunubi, haka kuma ta wurin biyayyar mutum guda, mutane da yawa za su zama masu adalci.
Kajti kakor so po neposlušnosti enega človeka grešni postali mnogi, tako bodo tudi po poslušnosti enega pravični postali mnogi.
20 An ba da dokar don mu ga yadda laifi yake da girma. Amma da zunubi ya ƙaru, sai alheri ya ƙaru sosai,
A postava je zravni tega prišla, da se pomnoži pregreha, a kjer se pregreha pomnoži, tam se še bolje poobilša milost,
21 domin, kamar yadda zunubi ya yi mulki cikin mutuwa, haka ma alheri yă yi mulki ta wurin adalci yă kuwa kawo rai madawwami ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu. (aiōnios g166)
Da bi, kakor je zakraljeval greh za smrt, tako tudi zakraljevala milost s pravico na večno življenje po Jezusu Kristusu Gospodu našem. (aiōnios g166)

< Romawa 5 >