< Romawa 5 >

1 Saboda haka, da yake an same mu marasa laifi ta wurin bangaskiya, muna da salama tare da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi,
Therefore being accepted as righteous through faith, we have peace with God through our Lord Jesus Christ;
2 ta wurinsa ne muka sami shiga wannan alherin da muke tsaye yanzu, ta wurin bangaskiya. Muna kuma farin ciki a begen ɗaukakar Allah.
through whom also we have had admission into this grace in which we stand, and rejoice in the hope of the glory which God will confer.
3 Ba haka kawai ba, amma muna kuma da farin ciki cikin shan wuyanmu, gama mun san cewa shan wuyan nan takan haifi jimiri;
And not only so, but we rejoice in afflictions also, knowing that affliction produceth endurance,
4 jimiri kuma yakan kawo hali mai kyau; hali mai kyau kuma yakan sa bege.
and endurance proof [[of faith]], and proof [[of faith giveth]] hope;
5 Bege kuwa ba ya ba mu kunya, domin Allah ya zuba ƙaunarsa a zukatanmu ta wurin Ruhu Mai Tsarkin da ya ba mu.
and hope will not disappoint us; because the love of God hath been shed abroad in our hearts by the Holy Spirit which hath been given to us.
6 Kun ga, a daidai lokaci, yayinda muke marasa ƙarfi, Kiristi ya mutu saboda waɗanda ba su san Allah ba.
For while we were yet without strength, in due season Christ died for the ungodly.
7 Da ƙyar wani yă mutu saboda mai adalci, ko da yake saboda mutumin kirki wani zai iya ƙarfin hali yă mutu.
Now hardly for a righteous man will one die; perhaps, however, for a benefactor one might even dare to die.
8 Amma Allah ya nuna mana ƙaunarsa a wannan. Tun muna masu zunubi tukuna, Kiristi ya mutu dominmu.
But God commendeth his love toward us, in that, while we were yet sinners, Christ died for us.
9 Da yake yanzu mun sami zama marasa laifi ta wurin jininsa, ashe kuwa za a cece mu daga fushin Allah ta wurinsa!
Much more then, being now accepted as righteous through his blood, we shall be saved through him from the [[coming]] wrath.
10 Gama in kuwa, sa’ad da muke abokan gāban Allah, aka sulhunta mu da shi ta wurin mutuwar Ɗansa, ashe, da yake an sulhunta mu, za mu sami ceto ta wurin ransa!
For if while enemies we were reconciled to God through the death of his Son, much more having been reconciled shall we be saved by his life;
11 Ba ma haka yake kawai ba, har muna farin ciki da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa yanzu muka sami sulhu.
and not this only, but also having joy in God through our Lord Jesus Christ, through whom we have now received the reconciliation.
12 Saboda haka, kamar yadda zunubi ya shigo duniya ta wurin mutum ɗaya, mutuwa kuma ta wurin zunubi, ta haka kuwa mutuwa ta shafi dukan mutane, domin dukan mutane sun yi zunubi.
So then as through one man sin entered into the world, and through sin death, and thus [[death]] came through unto all men, because all sinned—
13 Gama kafin a ba da doka, zunubi yana nan a duniya. Amma ba a lissafin zunubi inda babu doka.
(for all the time before the Law sin was in the world; but sin is not set to one's account when there is no law.
14 Duk da haka, mutuwa ta yi mulki tun Adamu har yă zuwa Musa, ta yi mulki har ma a kan waɗanda ba su yi zunubi ta wurin taka umarni kamar yadda Adamu ya yi ba. A wata hanya dai Adamu shi ne kwatancin wani mutumin nan mai zuwa.
Yet death reigned from Adam to Moses, even over those who had not sinned in the manner in which Adam transgressed; who is a type of him who was to come.—
15 Amma kyautan nan dabam take da laifin nan. Gama in mutane da yawa sun mutu saboda laifin mutum ɗayan nan, to, ai, alherin Allah da kuma kyautan nan mai zuwa ta wurin alherin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi, ya shafi mutane da yawa!
But the free gift was not as the transgression. For if through the offence of the one the many died, much more hath the grace of God, and the gift which is by the grace of the one man Jesus Christ, abounded to the many.
16 Kyautar Allah kuwa ba kamar sakamakon da ya bi zunubin mutum gudan nan ba ne, Hukuncin ya bi zunubin mutum gudan nan, ya kuma kawo hallaka, amma kyautar ta bi laifofin masu yawa ta kuma sa Allah ya gan mu a matsayin marasa laifi.
And the free gift is not like what happened through one man who sinned. For sentence of condemnation followed one offence; but the free gift is a justification after many offences.
17 Gama in, ta wurin laifin mutum ɗaya, mutuwa ta yi mulki ta wurin mutum ɗayan nan, ashe, waɗanda suka sami kyautar alherin Allah a yalwace da kuma kyautar adalci za su yi mulki a wannan rayuwa ta wurin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi.
For if by one trespass death reigned through the one man, much more will they who receive the abundance of grace and of the gift of righteousness reign in life through the one man Jesus Christ.)—
18 Saboda haka, kamar yadda sakamakon laifin mutum guda ya jawo hallaka ga dukan mutane, haka ma sakamakon aikin adalci guda ya sa Allah ya same mu marasa laifi, wannan kuwa kawo rai ga dukan mutane.
As then through one trespass all men have come under condemnation, so through one act of righteousness all obtain the gift of righteousness unto life.
19 Gama kamar yadda ta wurin rashin biyayyar mutum guda, mutane masu yawa suka zama masu zunubi, haka kuma ta wurin biyayyar mutum guda, mutane da yawa za su zama masu adalci.
For as through the disobedience of the one man the many were made sinners, so through the obedience of the one man will the many be made righteous.
20 An ba da dokar don mu ga yadda laifi yake da girma. Amma da zunubi ya ƙaru, sai alheri ya ƙaru sosai,
Moreover the law came in in addition, that the trespass might abound; but where sin abounded, grace abounded much more;
21 domin, kamar yadda zunubi ya yi mulki cikin mutuwa, haka ma alheri yă yi mulki ta wurin adalci yă kuwa kawo rai madawwami ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu. (aiōnios g166)
that as sin reigned in death, so grace might reign through righteousness to everlasting life, through Jesus Christ our Lord. (aiōnios g166)

< Romawa 5 >