< Romawa 4 >
1 To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
Kaj torej porečemo, da je Abraham naš oče našel po mesu?
2 In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
Kajti če se je Abraham iz del opravičil, ima hvalo, ali ne pri Bogu.
3 Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
Ker kaj pravi pismo? "Veroval pa je Abraham in zaračunilo se mu je za pravico."
4 To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
A tistemu, kteri dela, ne računi se plača po milosti, nego po dolgu;
5 Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
Tistemu pa, kteri ne dela, a veruje v tistega, kteri opravičuje nepobožnega, računi se njegova vera za pravico.
6 Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
Kakor tudi David pravi, da je blago človeku, komur Bog računi pravico brez del.
7 “Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
"Blagor jim, kterim so se odpustile nepostavnosti, in kterih grehi so se pokrili."
8 Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
"Blagor možu, kteremu ni zaračunil Gospod greha."
9 Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
Blago torej to le je v obrezi ali v neobrezi? Kajti pravimo, da se je zaračunila Abrahamu vera za pravico.
10 A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
Kako torej se mu je zaračunila? kedar je bil v obrezi ali v neobrezi? Ne v obrezi, nego v neobrezi.
11 Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
In prejel je znamenje obreze, pečat pravice vere, ktera je v neobrezi, da bi bil oče vseh, kteri verujejo v neobrezi, da bi se zaračunilo tudi njim za pravico;
12 Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
In da bi bil oče obreze ne samo tistim, kteri so iz obreze, nego tudi tistim, kteri hodijo po stopinjah vere v neobrezi očeta našega Abrahama;
13 Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
Kajti ni se dala s postavo obljuba Abrahamu ali njegovemu semenu, da bo dedič sveta, nego s pravico vere.
14 Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
Ker če so dediči ti, kteri so iz postave, prazna je vera in brez veljave obljuba.
15 domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
Kajti postava jezo napravlja, ker kjer ni postave, tudi ni prestopa.
16 Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
Za to iz vere, da po milosti, da bi bila trdna obljuba vsakemu semenu, ne samo tistemu, ktero je iz postave, nego tudi tistemu, ktero je iz vere Abrahama, kteri je oče vseh nas,
17 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
(Kakor je pisano: "Za očeta mnogih narodov sem te postavil.") pred Bogom, kteremu je veroval, kteri oživlja mrtve in kliče to, kar ni, kakor da je.
18 Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Kteri je veroval na up proti upu, da postane oče mnogih narodov poleg rečenega: "Tako bo seme tvoje."
19 Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
In ne oslabevši v veri ni premislil svojega telesa uže umrtvljenega, ker je imel blizu sto let, in mrtvosti maternice Sarine.
20 Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
A na obljubo Božjo ni posumnjil z nevero, nego ojačil se je v veri davši čast Bogu.
21 yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
In popolnoma prepričavši se, da je, kar je obljubil, mogoč tudi storiti.
22 Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
Za to se mu je tudi zaračunilo za pravico.
23 Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
Ali ni napisano samo za njega, da se mu je zaračunilo;
24 amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
Nego tudi za nas, kterim ima biti zaračunjeno, kteri verujemo v tistega, kteri je obudil Jezusa Gospoda našega iz mrtvih,
25 An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.
Kteri je bil dan za grehe naše in je vstal za opravičenje naše.