< Romawa 4 >

1 To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
Cóż tedy, rzeczemy, znalazł Abraham, ojciec nasz według ciała?
2 In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
Bo jeźli Abraham z uczynków jest usprawiedliwiony, ma się czem chlubić, ale nie u Boga.
3 Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
Albowiem cóż Pismo mówi? Uwierzył Abraham Bogu i przyczytano mu to za sprawiedliwość.
4 To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
A robiącemu zapłata nie bywa przyczytana podług łaski, ale podług długu;
5 Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
Nie robiącemu zaś, lecz wierzącemu w tego, który usprawiedliwia niepobożnego, przyczytana bywa wiara jego za sprawiedliwość.
6 Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
Jako i Dawid powiada, że błogosławieństwo człowieka jest, któremu Bóg przyczyta sprawiedliwość bez uczynków, mówiąc:
7 “Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
Błogosławieni, których odpuszczone są nieprawości, a których zakryte są grzechy;
8 Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
Błogosławiony mąż, któremu Pan grzechu nie przyczyta.
9 Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
To tedy błogosławieństwo tylko na obrzezkę przychodzi, czy też na nieobrzezkę? Gdyż mówimy, iż wiara Abrahamowi jest przyczytana za sprawiedliwość.
10 A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
Jakoż mu tedy jest przyczytano? Gdy był w obrzezce, czyli w nieobrzezce? Nie w obrzezce, ale w nieobrzezce.
11 Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
I przyjął znak obrzezki za pieczęć sprawiedliwości onej wiary, która była w nieobrzezce, na to, aby był ojcem wszystkich wierzących w nieobrzezce, aby i onym przyczytana była sprawiedliwość;
12 Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
I aby był ojcem obrzezki, nie tylko tych, którzy są z obrzezki, ale też i tych, którzy chodzą stopami wiary ojca naszego Abrahama, która była w nieobrzezce.
13 Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
Albowiem nie przez zakon się stała obietnica Abrahamowi albo nasieniu jego, aby był dziedzicem świata, ale przez sprawiedliwość wiary.
14 Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
Bo jeźli ci, którzy są z zakonu, dziedzicami są, tedyć zniszczała wiara i wniwecz się obróciła obietnica.
15 domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
Gdyż zakon gniew sprawuje; albowiem gdzie zakonu nie masz, tam ani przestępstwa.
16 Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
Przetoż z wiary jest dziedzictwo, aby było z łaski, i żeby była warowna obietnica wszystkiemu nasieniu, nie tylko temu, które jest z zakonu, ale i temu, które jest z wiary Abrahamowej, który jest ojcem nas wszystkich;
17 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
(Jako napisano: Ojcem wielu narodów wystawiłem cię) przed Bogiem, któremu uwierzył, który ożywia umarłe i który przywołuje te rzeczy, których nie masz, i jakoby były.
18 Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Który (Abraham) przeciwko nadziei w nadzieję uwierzył, że się stanie ojcem wielu narodów według tego, co mu powiedziano: Tak będzie nasienie twoje.
19 Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
A nie będąc słabym w wierze, nie patrzył na ciało swoje już obumarłe, mając około stu lat, ani na obumarły żywot Sary.
20 Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
O obietnicy tedy Bożej nie wątpił z niedowiarstwa; ale się umocnił wiarą i dał chwałę Bogu,
21 yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
Będąc też tego pewien, że cokolwiek on obiecał, mocen jest i uczynić.
22 Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
Przetoż przyczytano mu to za sprawiedliwość.
23 Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
A nie napisano tego dla niego samego, iż mu to przyczytano,
24 amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
Ale i dla nas, którym ma być przyczytano, którzy wierzymy w tego, który wzbudził Jezusa, Pana naszego, z martwych;
25 An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.
Który wydany jest dla grzechów naszych, a wstał z martwych dla usprawiedliwienia naszego.

< Romawa 4 >