< Romawa 4 >

1 To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
What shall we say then that Abraham our father obtained according to the flesh?
2 In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
for if Abraham were justified by works, he hath something to boast of; but this he hath not before God:
3 Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
for what saith the scripture? "Abraham believed God, and it was counted to him for righteousness."
4 To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
Now to him that worketh the reward is not reckoned as a favor, but as a debt:
5 Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
but to him that worketh not, but believeth on Him who justifieth the ungodly, his faith is accounted for righteousness.
6 Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
As David also describeth the blessedness of the man to whom: God imputeth righteousness without works, saying,
7 “Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
"Blessed are they whose iniquities are forgiven, and whose sins are covered:
8 Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
blessed is the man to whom the Lord imputeth not sin."
9 Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
Now is this blessedness upon the circumcised only, or upon the uncircumcised also? for we say that faith was accounted to Abraham for righteousness.
10 A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
How then was it accounted to him? when he was in circumcision, or in uncircumcision? Not in circumcision, but in uncircumcision.
11 Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
And he received the sign of circumcision as a seal of the righteousness of the faith which he had in uncircumcision: that he might be the father of all that believe though not circumcised, that righteousness may be imputed to them also:
12 Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
and the father of circumcision to those, who not only are of the circumcision, but also walk in the steps of that faith of our father Abraham, which he had in uncircumcision.
13 Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
For the promise made to Abraham, or to his seed, that he should be heir of the world, was not by the law, but by the righteousness of faith:
14 Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
for if they only that are of the law be heirs, faith is made useless, and the promise is become of no effect.
15 domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
Now the law worketh wrath; for where there is no law, there is no transgression.
16 Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
And therefore it is of faith, that it might be by grace, that so the promise might be sure to all the seed; not to that only which is of the law, but also to that which is of the faith of Abraham, who is the father of us all,
17 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
(as it is written, "I have made thee a father of many nations,") in the sight of Him whom he believed, even God, who giveth life to the dead, and calleth the things that are not as if they were:
18 Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
who against hope believed, with hope, that he should be the father of many nations, according to that which was said unto him, "So shall thy seed be."
19 Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
And not being weak in faith, he considered not his own body now dead, being about an hundred years old; nor the deadness of Sarah's womb.
20 Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
He hesitated not at the promise of God through unbelief: but was strong in faith, giving glory to God,
21 yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
and being fully persuaded, that what was promised He was able to perform:
22 Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
and therefore it was imputed to him for righteousness.
23 Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
Now it was not written on his account only, that it was imputed to him:
24 amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
but for our sakes also, to him it will be imputed, as we believe on Him that raised up Jesus our Lord from the dead:
25 An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.
who was delivered for our offences, and was raised again for our justification.

< Romawa 4 >