< Romawa 4 >
1 To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
What then shall we say that Abraham, our earthly forefather, has gained?
2 In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
For if he was held to be righteous on the ground of his actions, he has something to boast of; but not in the presence of God.
3 Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
For what says the Scripture? "And Abraham believed God, and this was placed to his credit as righteousness."
4 To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
But in the case of a man who works, pay is not reckoned a favour but a debt;
5 Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
whereas in the case of a man who pleads no actions of his own, but simply believes in Him who declares the ungodly free from guilt, his faith is placed to his credit as righteousness.
6 Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
In this way David also tells of the blessedness of the man to whose credit God places righteousness, apart from his actions.
7 “Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
"Blessed," he says, "are those whose iniquities have been forgiven, and whose sins have been covered over.
8 Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
Blessed is the man of whose sin the Lord will not take account."
9 Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
This declaration of blessedness, then, does it come simply to the circumcised, or to the uncircumcised as well? For Abraham's faith--so we affirm--was placed to his credit as righteousness.
10 A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
What then were the circumstances under which this took place? Was it after he had been circumcised, or before?
11 Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
Before, not after. And he received circumcision as a sign, a mark attesting the reality of the faith-righteousness which was his while still uncircumcised, that he might be the forefather of all those who believe even though they are uncircumcised--in order that this righteousness might be placed to their credit;
12 Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
and the forefather of the circumcised, namely of those who not merely are circumcised, but also walk in the steps of the faith which our forefather Abraham had while he was as yet uncircumcised.
13 Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
Again, the promise that he should inherit the world did not come to Abraham or his posterity conditioned by Law, but by faith-righteousness.
14 Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
For if it is the righteous through Law who are heirs, then faith is useless and the promise counts for nothing.
15 domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
For the Law inflicts punishment; but where no Law exists, there can be no violation of Law.
16 Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
All depends on faith, and for this reason--that acceptance with God might be an act of pure grace,
17 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
so that the promise should be made sure to all Abraham's true descendants; not merely to those who are righteous through the Law, but to those who are righteous through a faith like that of Abraham. Thus in the sight of God in whom he believed, who gives life to the dead and makes reference to things that do not exist, as though they did, Abraham is the forefather of all of us. As it is written, "I have appointed you to be the forefather of many nations."
18 Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Under utterly hopeless circumstances he hopefully believed, so that he might become the forefather of many nations, in agreement with the words "Equally numerous shall your posterity be."
19 Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
And, without growing weak in faith, he could contemplate his own vital powers which had now decayed--for he was nearly 100 years old--and Sarah's barrenness.
20 Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
Nor did he in unbelief stagger at God's promise, but became mighty in faith, giving glory to God,
21 yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
and being absolutely certain that whatever promise He is bound by He is able also to make good.
22 Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
For this reason also his faith was placed to his credit as righteousness.
23 Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
Nor was the fact of its being placed to his credit put on record for his sake only;
24 amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
it was for our sakes too. Faith, before long, will be placed to the credit of us also who are believers in Him who raised Jesus, our Lord, from the dead,
25 An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.
who was surrendered to death because of the offences we had committed, and was raised to life because of the acquittal secured for us.