< Romawa 3 >
1 To, mece ce ribar zama mutumin Yahuda, ko kuwa mene ne amfanin kaciya?
What then is the advantage of the Jew? Or what is the benefit of circumcision?
2 Akwai riba ƙwarai ta kowace hanya! Da farko dai, su ne aka danƙa wa kalmomin nan na Allah.
Much every way. First, because they were indeed entrusted with the oracles of God.
3 Amma a ce waɗansu ba su da bangaskiya fa? Rashin bangaskiyarsu nan zai shafe amincin Allah?
For what if some did not believe? Will their unbelief make the assurance of God ineffective?
4 Ko kaɗan! Bari Allah yă zama mai gaskiya, kowane mutum kuma yă zama maƙaryaci. Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Gama a tabbatar kana da gaskiya, sa’ad da ka yi magana, ka kuma yi nasara sa’ad da ka yi shari’a.”
May it not happen! But let it come to pass God is true, but every man a liar, as it is written, That thou may ever be justified in thy words, and may prevail when thou are criticized.
5 Amma in rashin adalcinmu ya bayyana adalcin Allah a fili, me za mu ce ke nan? Za mu ce Allah ya yi rashin adalci ke nan da ya saukar da fushinsa a kanmu? (Ina magana kamar yadda mutum zai yi ne.)
But if our unrighteousness commends the righteousness of God, what will we say? Is God unrighteous inflicting wrath? (I speak according to a man.)
6 Sam, ko kusa! Da a ce haka ne, ta yaya Allah zai shari’anta duniya?
May it not happen! Otherwise how will God judge the world?
7 Wani zai iya ce, “In a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka ƙara ɗaukaka shi, to, ta yaya zan zama mai zunubi, in ƙaryata tana kawo ɗaukaka ga Allah?”
For if by my lie, the truth of God abounded to his glory, why am I also still judged as sinful,
8 In haka ne, “Ba sai mu yi ta yin mugunta don yă zama hanyar samun nagarta ba”? Kamar yadda masu baƙar magana game da mu suna cewa wai haka muke faɗa. Tabbatacce za a hukunta irin waɗannan da hukuncin da ya dace da su.
and not (as we are slandered, and as some affirm us to say) that we may do evil so that good things may come (whose condemnation is just)?
9 To, me za mu ce ke nan? Mun fi su ke nan? Ina, ko kaɗan! Mun riga mun zartar cewa da Yahudawa da Al’ummai duk suna a ƙarƙarshin zunubi.
What then? Are we better? Not at all. For we already charged both Jews and Greeks to all be under sin,
10 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Babu wani mai adalci, babu ko ɗaya;
as it is written, There is no righteous man, not even one.
11 babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah.
There is no man who understands. There is no man who seeks God.
12 Duk sun kauce gaba ɗaya, sun zama marasa amfani; babu wani mai aikata nagarta, babu ko ɗaya.”
All turned away. Together they became useless. There is not a man who does goodness; there is not as much as one.
13 “Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne, harsunansu suna yin ƙarya.” “Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”
Their throat is an open grave. With their tongues they deceive. The poison of asps is under their lips,
14 “Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”
whose mouth is full of cursing and bitterness.
15 “Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;
Their feet are swift to shed blood.
16 hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,
Destruction and misery are in their ways,
17 ba su kuma san hanyar salama ba.”
and the way of peace they have not known.
18 “Babu tsoron Allah a idanunsu.”
There is no fear of God before their eyes.
19 Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah.
Now we know that as many things as the law says, it says to those in the law, so that every mouth may be stopped, and all the world may become accountable to God.
20 Saboda haka babu wanda Allah zai ce da shi mai adalci ta wurin kiyaye doka kawai; a maimako, ta wurin doka ne muke sane da zunubi.
Because from works of law no flesh will be made right before him, for through law is knowledge of sin.
21 Amma yanzu an bayyana wani adalci daga Allah, wannan adalcin bai danganta ga doka ba, Doka da Annabawa suna ba da shaida game da wannan adalci.
But now a righteousness of God has been manifested independent of law, being witnessed by the law and the prophets.
22 Wannan adalcin Allah yana zuwa ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi ga dukan waɗanda suka ba da gaskiya ne. Ba bambanci,
And the righteousness of God through faith in Jesus Christ is for all and upon all those who believe, for there is no distinction.
23 gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ɗaukakar Allah,
For all have sinned and come short of the glory of God,
24 an kuma kuɓutar da su kyauta ta wurin alherinsa bisa ga aikin fansar da ya zo ta wurin Yesu Kiristi.
being made righteous freely by his grace, through the redemption in Christ Jesus,
25 Allah ya miƙa Yesu Kiristi a matsayin hadayar kafara, ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya yi haka domin yă nuna adalcinsa, domin a cikin haƙurinsa bai hukunta zunuban da aka aikata a dā ba
whom God set forth an expiatory sacrifice through faith in his blood, for proof of his justice, because of the passing over of the sins that have formerly occurred
26 ya yi haka domin yă nuna adalcinsa a wannan lokaci, saboda yă zama mai adalci da mai kuɓutar da waɗanda suke ba da gaskiya a cikin Yesu.
(in the forbearance of God), for proof of his justice at the present time, for him to be righteous, and who makes the man from Jesus' faith righteous.
27 To, me za mu yi taƙama a kai? Babu wani abin da zamu yi taƙama a kai. A kan wace ƙa’ida ce za mu yi taƙama? Ta hanyar bin doka ne? A’a, sai dai ta wurin bangaskiya.
Where then is the boasting? It is excluded. By what law, of works? No, but by a law of faith.
28 Gama mun tsaya a kan cewa ta wurin bangaskiya ne ake kuɓutar da mutum, ba ta wurin kiyaye doka ba.
We therefore consider a man to be made righteous by faith independent of works of law.
29 Allah ɗin, Allahn Yahudawa ne kaɗai? Shi ba Allahn Al’ummai ba ne? I, shi Allahn Al’ummai ne ma,
Or is God of Jews only and not also of Gentiles? Yes, of Gentiles also,
30 da yake Allah ɗaya ne kaɗai, shi kuma zai kuɓutar da masu kaciya bisa ga bangaskiya da kuma marasa kaciya ta wurin wannan bangaskiya ɗin.
since God is one, who will make the man of circumcision righteous from faith, and the man of uncircumcision through faith.
31 To, za mu soke dokar saboda wannan bangaskiyar ne? Ko kaɗan! A maimako, sai ma tabbatar da ita muke yi.
Do we then make law void through faith? May it not happen! Instead, we establish law.