< Romawa 2 >
1 Saboda haka, kai da kake ba wa wani laifi, ba ka da wata hujja, gama a duk lokacin da kake ba wa wani laifi, kana hukunta kanka ne, domin kai da kake ba wa wani laifi kai ma kana aikata waɗannan abubuwa.
You are therefore without excuse, O man, whoever you are who sit in judgement upon others. For when you pass judgement on your fellow man, you condemn yourself; for you who sit in judgement upon others are guilty of the same misdeeds;
2 Yanzu mun san cewa hukuncin Allah a kan masu aikata waɗannan abubuwa daidai ne.
and we know that God's judgement against those who commit such sins is in accordance with the truth.
3 Saboda haka sa’ad da kai mutum kurum, kana ba su laifi, duk da haka kana aikata abubuwan nan, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne?
And you who pronounce judgement upon those who do such things although your own conduct is the same as theirs--do you imagine that you yourself will escape unpunished when God judges?
4 Ko kuma kana rena wadatar alherinsa, haƙurinsa, da kuma jimrewarsa ne ba tare da sanin cewa alherin Allah yana kai ka ga tuba ba ne?
Or is it that you think slightingly of His infinite goodness, forbearance and patience, unaware that the goodness of God is gently drawing you to repentance?
5 Amma saboda taurinkanka da zuciyarka marar tuba, kana tara wa kanka fushi a ranar fushin Allah, sa’ad da za a bayyana hukuncinsa mai adalci.
The fact is that in the stubbornness of your impenitent heart you are treasuring up against yourself anger on the day of Anger--the day when the righteousness of God's judgements will stand revealed.
6 Allah, “Zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikin da ya yi.”
To each man He will make an award corresponding to his actions;
7 Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami. (aiōnios )
to those on the one hand who, by lives of persistent right-doing, are striving for glory, honour and immortality, the Life of the Ages; (aiōnios )
8 Amma ga waɗanda suke sonkai waɗanda suke ƙin gaskiya suke kuma bin mugunta, akwai fushi da haushi dominsu.
while on the other hand upon the self-willed who disobey the truth and obey unrighteousness will fall anger and fury, affliction and awful distress,
9 Akwai wahala da baƙin ciki ga duk mutumin da yake aikata mugunta, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai,
coming upon the soul of every man and woman who deliberately does wrong--upon the Jew first, and then upon the Gentile;
10 amma akwai ɗaukaka, girma da salama ga duk mutumin da yake aikata alheri, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai.
whereas glory, honour and peace will be given to every one who does what is good and right--to the Jew first and then to the Gentile.
11 Gama Allah ba ya nuna bambanci.
For God pays no attention to this world's distinctions.
12 Duk waɗanda suka yi zunubi a rashi sanin doka, a rashin doka za su hallaka, waɗanda kuma suka yi zunubi ƙarƙashin doka, a ƙarƙashin doka za a hukunta su.
For all who have sinned apart from the Law will also perish apart from the Law, and all who have sinned whilst living under the Law, will be judged by the Law.
13 Gama ba masu jin dokar ne suke da adalci a gaban Allah ba, amma waɗanda suke yin biyayya da dokar, su za a ce da su masu adalci.
It is not those that merely hear the Law read who are righteous in the sight of God, but it is those that obey the Law who will be pronounced righteous.
14 Tabbatacce, sa’ad da Al’ummai, waɗanda ba su da dokar, suka aikata abubuwan da dokar take bukata, abubuwan sun zama doka ke nan gare su, ko da yake ba su da dokar.
For when Gentiles who have no Law obey by natural instinct the commands of the Law, they, without having a Law, are a Law to themselves;
15 To, da yake sun nuna cewa abubuwan da dokar take bukata suna a rubuce a zukatansu, lamirinsu yana kuma ba da shaida, tunaninsu kuwa yanzu yana zarginsu ko kuma yana kāre su.
since they exhibit proof that a knowledge of the conduct which the Law requires is engraven on their hearts, while their consciences also bear witness to the Law, and their thoughts, as if in mutual discussion, accuse them or perhaps maintain their innocence--
16 Wannan zai faru a ranar da Allah ta wurin Yesu Kiristi zai shari’anta ɓoyayyun abubuwan da mutane suka yi, yadda bisharata ta furta.
on the day when God will judge the secrets of men's lives by Jesus Christ, as declared in the Good News as I have taught it.
17 To, kai, da kake kiran kanka mutumin Yahuda; in kana dogara ga doka kana kuma taƙama da dangantakarka da Allah;
And since you claim the name of Jew, and find rest and satisfaction in the Law, and make your boast in God,
18 in ka san nufinsa ka kuma amince da abin da yake mafifici domin an koyar da kai bisa ga doka;
and know the supreme will, and can test things that differ--being a man who receives instruction from the Law--
19 in ka tabbata cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga waɗanda suke cikin duhu,
and have persuaded yourself that, as for you, you are a guide to the blind, a light to those who are in darkness,
20 mai koyar da masu wauta, malamin jarirai, domin a cikin dokar ce akwai sani da gaskiya
a schoolmaster for the dull and ignorant, a teacher of the young, because in the Law you possess an outline of real knowledge and an outline of the truth:
21 to, kai mai koya wa waɗansu, ba kanka kake koya wa ba? Kai da kake wa’azi kada a yi sata, kana sata?
you then who teach your fellow man, do you refuse to teach yourself? You who cry out against stealing, are you yourself a thief?
22 Kai da kake cewa wa mutane kada su yi zina, kana yin zina? Kai da kake ƙyamar gumaka, kana wa haikali fashi?
You who forbid adultery, do you commit adultery? You who loathe idols, do you plunder their temples?
23 Kai da kake taƙama da doka, kana nuna rashin bangirma ga Allah ta wurin karya dokar?
You who make your boast in the Law, do you offend against its commands and so dishonour God?
24 Kamar yadda yake a rubuce, “Ana saɓon sunan Allah a cikin Al’ummai saboda ku.”
For the name of God is blasphemed among the Gentile nations because of you, as Holy Writ declares.
25 Kaciya tana da amfani in kana kiyaye dokar, amma in kana karya dokar, ka zama kamar ba a yi maka kaciya ba.
Circumcision does indeed profit, if you obey the Law; but if you are a Law-breaker, the fact that you have been circumcised counts for nothing.
26 In marasa kaciya suna kiyaye dokar, ashe, ba za a ɗauke su kamar an yi musu kaciya ba?
In the same way if an uncircumcised man pays attention to the just requirements of the Law, shall not his lack of circumcision be overlooked, and,
27 Wanda ba shi da kaciya ta jiki duk da haka yana biyayya da dokar zai iya hukunta ka, kai da kake karya dokar, ko da yake kana da rubutaccen tsarin dokar an kuma yi maka kaciya.
although he is a Gentile by birth, if he scrupulously obeys the Law, shall he not sit in judgement upon you who, possessing, as you do, a written Law and circumcision, are yet a Law-breaker?
28 Mutum ba mutumin Yahuda ba ne in shi mutumin Yahuda ne kawai a jiki, haka kuma kaciya ba a waje ko a jiki kawai ba.
For the true Jew is not the man who is simply a Jew outwardly, and true circumcision is not that which is outward and bodily.
29 A’a, mutum mutumin Yahuda ne in shi mutumin Yahuda ne a zuci; kuma kaciya ita ce kaciya ta zuci, ta wurin Ruhu, ba ta wurin rubutaccen doka ba. Irin wannan mutum yana samun yabo daga Allah ne, ba ɗan adam ba.
But the true Jew is one inwardly, and true circumcision is heart-circumcision--not literal, but spiritual; and such people receive praise not from men, but from God.