< Romawa 2 >

1 Saboda haka, kai da kake ba wa wani laifi, ba ka da wata hujja, gama a duk lokacin da kake ba wa wani laifi, kana hukunta kanka ne, domin kai da kake ba wa wani laifi kai ma kana aikata waɗannan abubuwa.
Wherefore thou art without excuse, O man that judgest, whoever thou art. For wherein thou judgest another, thou condemnest thyself; for thou that judgest doest the same things.
2 Yanzu mun san cewa hukuncin Allah a kan masu aikata waɗannan abubuwa daidai ne.
But we know that the judgment of God is according to truth against those who practise such things.
3 Saboda haka sa’ad da kai mutum kurum, kana ba su laifi, duk da haka kana aikata abubuwan nan, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne?
And dost thou suppose, O man, who art judging those who do such things, and art thyself doing the same, that thou wilt escape the judgment of God?
4 Ko kuma kana rena wadatar alherinsa, haƙurinsa, da kuma jimrewarsa ne ba tare da sanin cewa alherin Allah yana kai ka ga tuba ba ne?
Or dost thou despise the riches of his goodness and forbearance and longsuffering, not knowing that the goodness of God is leading thee to repentance?
5 Amma saboda taurinkanka da zuciyarka marar tuba, kana tara wa kanka fushi a ranar fushin Allah, sa’ad da za a bayyana hukuncinsa mai adalci.
But according to thy hardness and impenitent heart, thou art treasuring up for thyself wrath against the day of wrath and of the manifestation of the righteous judgment of God,
6 Allah, “Zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikin da ya yi.”
who will render to every one according to his works;
7 Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami. (aiōnios g166)
everlasting life to those who by patient continuance in well-doing seek for glory, and honor, and incorruption; (aiōnios g166)
8 Amma ga waɗanda suke sonkai waɗanda suke ƙin gaskiya suke kuma bin mugunta, akwai fushi da haushi dominsu.
but to those who are contentious, and disobedient to the truth; but obey unrighteousness, there will be wrath and indignation.
9 Akwai wahala da baƙin ciki ga duk mutumin da yake aikata mugunta, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai,
Tribulation and distress will be upon every soul of man whose works are evil, of the Jew first, and also of the Greek;
10 amma akwai ɗaukaka, girma da salama ga duk mutumin da yake aikata alheri, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai.
but glory, honor, and peace, to every one whoso works are good, to the Jew first, and also to the Greek.
11 Gama Allah ba ya nuna bambanci.
For there is no respect of persons with God.
12 Duk waɗanda suka yi zunubi a rashi sanin doka, a rashin doka za su hallaka, waɗanda kuma suka yi zunubi ƙarƙashin doka, a ƙarƙashin doka za a hukunta su.
For as many as have sinned without a law, will also perish without a law; and as many as have sinned under a law, will be judged by a law,
13 Gama ba masu jin dokar ne suke da adalci a gaban Allah ba, amma waɗanda suke yin biyayya da dokar, su za a ce da su masu adalci.
for it is not the hearers of a law who are righteous before God, but the doers of a law will be accounted righteous; —
14 Tabbatacce, sa’ad da Al’ummai, waɗanda ba su da dokar, suka aikata abubuwan da dokar take bukata, abubuwan sun zama doka ke nan gare su, ko da yake ba su da dokar.
for when the gentiles, who have no law, do by nature what is required by the Law, these, having no law, are a law to themselves;
15 To, da yake sun nuna cewa abubuwan da dokar take bukata suna a rubuce a zukatansu, lamirinsu yana kuma ba da shaida, tunaninsu kuwa yanzu yana zarginsu ko kuma yana kāre su.
since they show that what the Law requireth is written in their hearts, their conscience bearing witness, and their thoughts in turn accusing or defending them; —
16 Wannan zai faru a ranar da Allah ta wurin Yesu Kiristi zai shari’anta ɓoyayyun abubuwan da mutane suka yi, yadda bisharata ta furta.
in the day when God shall judge the secrets of men by Jesus Christ, according to the gospel which I have preached.
17 To, kai, da kake kiran kanka mutumin Yahuda; in kana dogara ga doka kana kuma taƙama da dangantakarka da Allah;
But if thou art called a Jew, and restest on the Law, and makest thy boast of God,
18 in ka san nufinsa ka kuma amince da abin da yake mafifici domin an koyar da kai bisa ga doka;
and knowest his will, and approvest the things that are more excellent, being instructed out of the Law;
19 in ka tabbata cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga waɗanda suke cikin duhu,
and art confident that thou thyself art a guide of the blind, a light to those who are in darkness,
20 mai koyar da masu wauta, malamin jarirai, domin a cikin dokar ce akwai sani da gaskiya
an instructor of those who lack wisdom, a teacher of babes, having the form of knowledge and of the truth in the Law, —
21 to, kai mai koya wa waɗansu, ba kanka kake koya wa ba? Kai da kake wa’azi kada a yi sata, kana sata?
dost thou then who teachest another, not teach thyself? Thou who proclaimest that others should not steal, dost thou steal?
22 Kai da kake cewa wa mutane kada su yi zina, kana yin zina? Kai da kake ƙyamar gumaka, kana wa haikali fashi?
Dost thou who forbiddest to commit adultery, thyself commit adultery? Thou that abhorrest idols, dost thou rob temples?
23 Kai da kake taƙama da doka, kana nuna rashin bangirma ga Allah ta wurin karya dokar?
Dost thou who boastest of the Law, dishonor God by breaking the Law?
24 Kamar yadda yake a rubuce, “Ana saɓon sunan Allah a cikin Al’ummai saboda ku.”
For, as it is written, “the name of God is on your account blasphemed among the gentiles.”
25 Kaciya tana da amfani in kana kiyaye dokar, amma in kana karya dokar, ka zama kamar ba a yi maka kaciya ba.
For circumcision is indeed a benefit to thee, if thou keep the Law; but if thou art a breaker of the Law, thy circumcision hath become uncircumcision.
26 In marasa kaciya suna kiyaye dokar, ashe, ba za a ɗauke su kamar an yi musu kaciya ba?
If then he who is uncircumcised keep the precepts of the Law, shall not he though uncircumcised be regarded as circumcised?
27 Wanda ba shi da kaciya ta jiki duk da haka yana biyayya da dokar zai iya hukunta ka, kai da kake karya dokar, ko da yake kana da rubutaccen tsarin dokar an kuma yi maka kaciya.
Yea, those who are by nature uncircumcised, if they perform the law, will judge thee, who having a written Law and circumcision, art a breaker of the Law.
28 Mutum ba mutumin Yahuda ba ne in shi mutumin Yahuda ne kawai a jiki, haka kuma kaciya ba a waje ko a jiki kawai ba.
For he is not a Jew, who is one outwardly, nor is that circumcision, which is outward, in the flesh;
29 A’a, mutum mutumin Yahuda ne in shi mutumin Yahuda ne a zuci; kuma kaciya ita ce kaciya ta zuci, ta wurin Ruhu, ba ta wurin rubutaccen doka ba. Irin wannan mutum yana samun yabo daga Allah ne, ba ɗan adam ba.
but he is a Jew who is one inwardly; and circumcision is of the heart, spiritual, not literal, whose praise is not of men, but of God.

< Romawa 2 >