< Romawa 2 >

1 Saboda haka, kai da kake ba wa wani laifi, ba ka da wata hujja, gama a duk lokacin da kake ba wa wani laifi, kana hukunta kanka ne, domin kai da kake ba wa wani laifi kai ma kana aikata waɗannan abubuwa.
Derfor er du uden Undskyldning, o Menneske! hvem du end er, som dømmer; thi idet du dømmer den anden, fordømmer du dig selv; thi du, som dømmer, øver det samme.
2 Yanzu mun san cewa hukuncin Allah a kan masu aikata waɗannan abubuwa daidai ne.
Vi vide jo, at Guds Dom er, stemmende med Sandhed, over dem, som øve saadanne Ting.
3 Saboda haka sa’ad da kai mutum kurum, kana ba su laifi, duk da haka kana aikata abubuwan nan, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne?
Men du, o Menneske! som dømmer dem, der øve saadanne Ting, og selv gør dem, mener du dette, at du skal undfly Guds Dom?
4 Ko kuma kana rena wadatar alherinsa, haƙurinsa, da kuma jimrewarsa ne ba tare da sanin cewa alherin Allah yana kai ka ga tuba ba ne?
Eller foragter du hans Godheds og Taalmodigheds og Langmodigheds Rigdom og ved ikke, at Guds Godhed leder dig til Omvendelse?
5 Amma saboda taurinkanka da zuciyarka marar tuba, kana tara wa kanka fushi a ranar fushin Allah, sa’ad da za a bayyana hukuncinsa mai adalci.
Men efter din Haardhed og dit ubodfærdige Hjerte samler du dig selv Vrede paa Vredens og Guds retfærdige Doms Aabenbarelses Dag,
6 Allah, “Zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikin da ya yi.”
han, som vil betale enhver efter hans Gerninger:
7 Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami. (aiōnios g166)
dem, som med Udholdenhed i god Gerning søge Ære og Hæder og Uforkrænkelighed, et evigt Liv; (aiōnios g166)
8 Amma ga waɗanda suke sonkai waɗanda suke ƙin gaskiya suke kuma bin mugunta, akwai fushi da haushi dominsu.
men over dem, som søge deres eget og ikke lyde Sandheden, men adlyde Uretfærdigheden, skal der komme Vrede og Harme.
9 Akwai wahala da baƙin ciki ga duk mutumin da yake aikata mugunta, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai,
Trængsel og Angest over hvert Menneskes Sjæl, som øver det onde, baade en Jødes først og en Grækers;
10 amma akwai ɗaukaka, girma da salama ga duk mutumin da yake aikata alheri, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai.
men Ære og Hæder og Fred over hver den, som gør det gode, baade en Jøde først og en Græker!
11 Gama Allah ba ya nuna bambanci.
Thi der er ikke Persons Anseelse hos Gud.
12 Duk waɗanda suka yi zunubi a rashi sanin doka, a rashin doka za su hallaka, waɗanda kuma suka yi zunubi ƙarƙashin doka, a ƙarƙashin doka za a hukunta su.
Thi alle de, som have syndet uden Loven, de skulle ogsaa fortabes uden Loven; og alle de, som have syndet under Loven, de skulle dømmes ved Loven;
13 Gama ba masu jin dokar ne suke da adalci a gaban Allah ba, amma waɗanda suke yin biyayya da dokar, su za a ce da su masu adalci.
thi ikke Lovens Hørere ere retfærdige for Gud, men Lovens Gørere skulle retfærdiggøres —
14 Tabbatacce, sa’ad da Al’ummai, waɗanda ba su da dokar, suka aikata abubuwan da dokar take bukata, abubuwan sun zama doka ke nan gare su, ko da yake ba su da dokar.
thi naar Hedninger, som ikke have Loven, af Naturen gøre, hvad Loven kræver, da ere disse, uden at have Loven, sig selv en Lov;
15 To, da yake sun nuna cewa abubuwan da dokar take bukata suna a rubuce a zukatansu, lamirinsu yana kuma ba da shaida, tunaninsu kuwa yanzu yana zarginsu ko kuma yana kāre su.
de vise jo Lovens Gerning skreven i deres Hjerter, idet deres Samvittighed vidner med, og Tankerne indbyrdes anklage eller ogsaa forsvare hverandre —
16 Wannan zai faru a ranar da Allah ta wurin Yesu Kiristi zai shari’anta ɓoyayyun abubuwan da mutane suka yi, yadda bisharata ta furta.
paa den Dag, da Gud vil dømme Menneskenes skjulte Færd ifølge mit Evangelium ved Jesus Kristus.
17 To, kai, da kake kiran kanka mutumin Yahuda; in kana dogara ga doka kana kuma taƙama da dangantakarka da Allah;
Men naar du kalder dig Jøde og forlader dig trygt paa Loven og roser dig af Gud
18 in ka san nufinsa ka kuma amince da abin da yake mafifici domin an koyar da kai bisa ga doka;
og kender hans Villie og værdsætter de forskellige Ting, idet du undervises af Loven,
19 in ka tabbata cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga waɗanda suke cikin duhu,
og trøster dig til at være blindes Vejleder, et Lys for dem, som ere i Mørke,
20 mai koyar da masu wauta, malamin jarirai, domin a cikin dokar ce akwai sani da gaskiya
uforstandiges Opdrager, umyndiges Lærer, idet du i Loven har Udtrykket for Erkendelsen og Sandheden, —
21 to, kai mai koya wa waɗansu, ba kanka kake koya wa ba? Kai da kake wa’azi kada a yi sata, kana sata?
du altsaa, som lærer andre, du lærer ikke dig selv! Du, som prædiker, at man ikke maa stjæle, du stjæler!
22 Kai da kake cewa wa mutane kada su yi zina, kana yin zina? Kai da kake ƙyamar gumaka, kana wa haikali fashi?
Du, som siger, at man ikke maa bedrive Hor, du bedriver Hor! Du, som føler Afsky for Afguderne, du øver Tempelran!
23 Kai da kake taƙama da doka, kana nuna rashin bangirma ga Allah ta wurin karya dokar?
Du, som roser dig af Loven, du vanærer Gud ved Overtrædelse af Loven!
24 Kamar yadda yake a rubuce, “Ana saɓon sunan Allah a cikin Al’ummai saboda ku.”
Thi „for eders Skyld bespottes Guds Navn iblandt Hedningerne‟, som der er skrevet.
25 Kaciya tana da amfani in kana kiyaye dokar, amma in kana karya dokar, ka zama kamar ba a yi maka kaciya ba.
Thi vel gavner Omskærelse, om du holder Loven; men er du Lovens Overtræder, da er din Omskærelse bleven til Forhud.
26 In marasa kaciya suna kiyaye dokar, ashe, ba za a ɗauke su kamar an yi musu kaciya ba?
Dersom nu Forhuden holder Lovens Forskrifter, vil da ikke hans Forhud blive regnet som Omskærelse?
27 Wanda ba shi da kaciya ta jiki duk da haka yana biyayya da dokar zai iya hukunta ka, kai da kake karya dokar, ko da yake kana da rubutaccen tsarin dokar an kuma yi maka kaciya.
Og naar den af Natur uomskaarne opfylder Loven, skal han dømme dig, som med Bogstav og Omskærelse er Lovens Overtræder.
28 Mutum ba mutumin Yahuda ba ne in shi mutumin Yahuda ne kawai a jiki, haka kuma kaciya ba a waje ko a jiki kawai ba.
Thi ikke den er Jøde, som er det i det udvortes, ej heller er det Omskærelse, som sker i det udvortes, i Kød;
29 A’a, mutum mutumin Yahuda ne in shi mutumin Yahuda ne a zuci; kuma kaciya ita ce kaciya ta zuci, ta wurin Ruhu, ba ta wurin rubutaccen doka ba. Irin wannan mutum yana samun yabo daga Allah ne, ba ɗan adam ba.
men den, som indvortes er Jøde, og Hjertets Omskærelse i Aand, ikke i Bogstav — hans Ros er ikke af Mennesker, men af Gud.

< Romawa 2 >