< Romawa 16 >

1 Ina gabatar muku da’yar’uwarmu Fibi, baranyar ikkilisiya a Kenkireya.
Ngunapinga mwaamanyanje alumbu bhetu a Poebha, bhatumishi bha likanisha lya ku Kenkelea.
2 Ina roƙonku ku karɓe ta a cikin Ubangiji yadda ya dace a karɓi tsarkaka a kuma ba ta kowane irin taimakon da take bukata daga wurinku, gama ta zama mai taimako ƙwarai ga mutane masu yawa, haɗe da ni ma.
Mwaaposhelanje kwa ligongo lya Bhakulungwa malinga shiikupinjikwa kubhandunji bha ukonjelo. Mwaajangutilanje kwa shoshowe shibhapinga kunnjuganga, pabha na bhalabho bhashikwaajangutilanga bhandu bhabhagwinji pamo na nne.
3 Ku gai da Firiskila da Akwila, abokan aikina cikin Kiristi Yesu.
Mwaashalimianje a Pilishika na a Akula, bhatumishi ajangunji bha a Kilishitu Yeshu.
4 Sun yi kasai da ransu saboda ni. Ba ni kaɗai nake musu godiya ba amma har ma da dukan ikkilisiyoyin Al’ummai.
Bhene bhanganyabho bhapingaga bhulagwanga kwa ligongo lyangu nne. Ngunakwaatendelanga eja, nngabha nne jikape, ikabhe na makanisha gowe ga bhandu bha ilambo ina.
5 Ku kuma gai da ikkilisiyar da take haɗuwa a gidansu. Ku gai da ƙaunataccen abokina Efenetus, wanda ya zama na farko a karɓar Kiristi a lardin Asiya.
Na kabhili, shalamu ku bhandunji bha likanisha bhaimananga nnyumba jabhonji. Shalamu ambwiga ajangu a Epainito, bhali bha ndandubho kwaakulupalila a Kilishitu, nshilambo sha Ashia.
6 Ku gai da Maryamu wadda ta yi muku aiki tuƙuru.
Shalamu shabho a Malia bhatumbile kamula liengo kwa ligongo lyenu mmanganya.
7 Ku gai da Anduronikus da Yuniyas, dangina waɗanda aka daure a kurkuku tare da ni. Su fitattu ne sosai a cikin manzanni, sun riga ni zama masu bin Kiristi.
Shalamu kwa a Ndoloniko na a Yonashi, ashaalongo ajangunji bhatabhilwenje pamo na nne, bhandunji bha manyika munkumbi gwa ashimitume bha a Yeshu, bhalinginji Bhakilishitu nne nganabhe kubha Nankilishitu.
8 Ku gai da Amfiliyatus, ƙaunataccena a cikin Ubangiji.
Shalamu kwa a Ampiliato, ambwiga ajangu nkulundana na Bhakulungwa.
9 Ku gai da Urbanus, abokin aikinmu cikin Kiristi, da kuma ƙaunataccen abokina Sitakis.
Shalamu kwa a Alubhanushi, bhatumishi ajangu bha a Kilishitu, shalamu ambwiga ajangu a Shitaku.
10 Ku gai da Afelles wanda amincinsa cikin Kiristi tabbatacce ne. Ku gai da iyalin gidan Aristobulus.
Shalamu kwa a Apelishi, kulupalika kwabho kwa a Yeshu kumanyishe. Shalamu bhowenji bhalinginji nnyumba ja Alishitobhula.
11 Ku gai da ɗan’uwana, Hirodiyon. Ku gai da iyalin gidan Narkissus da suke cikin Ubangiji.
Shalamu alongo ajangu a Elodiana, shalamu bhandunji bhowe bha nnyumba ja a Nakishiushi, bhakwaakulupalilanga Bhakulungwa.
12 Ku gai da Tiryifena da Tiryifosa, matan nan da suke aiki tuƙuru cikin Ubangiji. Ku gai da ƙaunatacciyata Fersis, wata matan da ta yi aiki tuƙuru cikin Ubangiji.
Shalamu shabhonji a Tulupina na a Tuluposha bhanabhakongwe bhaakamulanga liengo lya Bhakulungwa. Shalamu jabho ambwiga ajangu a Pelishishi, na bhalabho bhakongwe bhakamwile liengo kwa tumbila kwa ligongo lya Bhakulungwa.
13 Ku gai da Rufus zaɓaɓɓe cikin Ubangiji, da kuma mahaifiyarsa, wadda ta zama kamar mahaifiya a gare ni.
Shalamu shabho a Lupo, bhakamula liengo kwa tumbila na anyinabhabho numbe nne bhungwaashema mama.
14 Ku gai da Asinkiritus, Filegon, Hermes, Faturobas, Hermas da kuma’yan’uwan da suke tare da su.
Shalamu shabhonji Ashinkilito na a Pilegoni na a Eme na a Patulobhashi na a Ema na ashaapwetu bhalinginji pamo na bhene bhanganyabho.
15 Ku gai da Filologus, Yuliya, Nereyus da’yar’uwarsa, da kuma Olimfas da dukan tsarkakan da suke tare da su.
Shalamu yabhonji a Pilologo na a Julia na a Neliashi na alumbu bhabho, na a Olimpa na bhandunji bha ukonjelo bhalinginji pamo na bhene bhanganyabho.
16 Ku gaggai da juna da sumba mai tsarki. Dukan ikkilisiyoyin Kiristi suna gaishe ku.
Nshalimiananje kwa ukonjelo. Shalamu shenunji kukopoka ku bhandu bha makanisha gowe ga a Kilishitu.
17 Ina roƙonku,’yan’uwa, ku yi hankali fa da masu raba tsakani, saɓanin koyarwar da kuka koya, suna sa tuntuɓe. Ku yi nesa da su.
Ashaalongo ajangunji, ngunakunshondelesheyanga mwiiteiganje na bhene bhakumbuyanga ya malekano nikwaabhulayanga bhananji kulebha, nileka majiganyo gunnjigenywenje. Mwiepuyanje na bhene bhandunjibho,
18 Gama irin waɗannan mutane ba sa bautar Ubangijinmu Kiristi, sai dai cikinsu. Ta wurin yaudara da kuma daɗin baki, suna ruɗin marasa wayo.
pabha bhandunji bha nneyo bhakakwatumishilanga Bhakulungwa bhetu a Kilishitu, ikabhe mapitiu gabhonji ashaayene. Kwa malobhe gabhonji ga nong'aya na kwiikonjeleya bhanapuganyanga mitima ja bhandunji bhakakushimanyanga shindu.
19 Kowa ya riga ya ji game da biyayyarku, don haka ina cike da farin ciki game da ku; amma ina so ku zama masu hikima game da abin da yake nagari, ku kuma zama marasa laifi ga abin da yake mugu.
Bhandu bhowe bhapilikenenje ga kunda kwenunji, kwa nneyo nnanonyelanga. Ikabheje pungupinga nkolanje lunda kwa indu ya mmbone na nnaputukanje kwa indu yangali ya mmbone.
20 Allah na salama zai tattake Shaiɗan ba da daɗewa ba yă kuma sa shi a ƙarƙashin sawunku. Alherin Ubangijinmu Yesu kuma yă kasance tare da ku.
Na a Nnungu bha ulele shangupe shibhamponde Lishetani pamakongono genunji. Nema ja Bhakulungwa bhetu a Yeshu Kilishitu jibhe na mmanganya.
21 Timoti, abokin aikina, yana gai da ku, haka ma Lusiyus, Yason, da Sosifater, dangina.
A Timoteo bhatumishi ajangu bhanakunnamushilanga. Na a Lukio na a Yashoni na a Shoshipateli ashaalongo ajangunji, bhanakunnamushilanga.
22 Ni, Tertiyus, wanda ya rubuta wannan wasiƙa, ina gai da ku cikin Ubangiji.
Na nne a Tetio, ngujandika jene bhaluwa jino, ngunakunnamushilanga kwa lina lya Bhakulungwa.
23 Gayus, mai masauƙina, mai kuma saukar da dukan’yan Ikkilisiya, yana gaishe ku. Erastus, mai bi da ayyukan jama’ar gari, da kuma ɗan’uwanmu Kwartus, suna gaishe ku.
A Gayo, bhayene mui bhamboshele na bhandu bhowe bha likanisha bhaimananga nnyumba jabho, bhanakunnamushilanga. A Elashito, bhaagoya mmbiya bha shilambo na a Kwatushi bhanakunshalimianga.
Nema ja Bhakulungwa bhetu a Yeshu Kilishitu jibhe na mmowenji. Amina.
25 Ɗaukaka ta tabbata ga mai ikon ƙarfafa ku bisa ga bisharata, bisa ga wa’azin Yesu Kiristi, wadda ta gare ta ne aka bayyana asirin nan da yake ɓoye tun fil azal, (aiōnios g166)
Bhai, nnaino bhakuywe a Nnungu! Bhalabho bhanakombola kunshimilikanga Nngani ja Mmbone ja a Yeshu Kilishitu jinungwiye jila, malinga shiishite manyika indu ya nng'iyo, ikamanyikaga pitipiti, (aiōnios g166)
26 amma yanzu kuwa aka bayyana, aka kuma sanar ta wurin rubuce-rubucen annabawa bisa ga umarnin Allah madawwami, domin dukan al’ummai su gaskata su kuma yi masa biyayya (aiōnios g166)
ikabheje nnaino imanyishe kwa majandiko ga ashinkulondola bha a Nnungu, kwa amuli ja a Nnungu bha pitipiti, nkupinga bhandu bha ilambo yowe bhakulupalilanje na kunda. (aiōnios g166)
27 ɗaukaka ta tabbata har abada ga Allah, wanda shi ne kaɗai mai hikima ta wurin Yesu Kiristi! Amin. (aiōn g165)
Bhai, a Nnungu bhakwete lunda jikape, bhakuywe pitipiti kupitila a Yeshu Kilishitu. Amina. (aiōn g165)

< Romawa 16 >