< Romawa 15 >
1 Mu da muke da ƙarfi ya kamata mu yi haƙuri da kāsawar marasa ƙarfi ba kawai mu gamshi kanmu ba.
lino twevano tuli ni ngufu tunoghile kukuvutola uvuvote vote vwa vano vavote vote, neke natunoghile kujivelelesia jusue.
2 Ya kamata kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai don kyautata zamansa domin kuma yă gina shi.
umuunhu ghweni mu lyusue amughanaghe un'jake ulwakuva lwe lunono ku vufumbue vwa kukunkangasia.
3 Gama ko Kiristi ma bai gamshi kansa ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zage-zagen da waɗansu suka yi maka, duk sun fāɗo a kaina.”
ulwakuva naju Kilisite nakajiloghelisie jujuo neke pepano jilyale ndavule jilembilue kuuti, “amaligho gha vala vano vakakulighile ghanyaghile une”.
4 Gama duk abin da aka rubuta a dā an rubuta ne domin yă koya mana, don ta wurin jimrewa da kuma ƙarfafawar Nassosi mu kasance da bege.
ku kyokyoni kino kilongwile kulembua, kilyalembilue kwa kutuvulanisia ku gila kuuti kukilila ulugudo na kukilila kukangasivua amoojo na malembe twale tuuva nu lukangasio.
5 Bari Allah mai ba da haƙuri da kuma ƙarfafawa yă ba ku ruhun haɗinkai da juna yayinda kuke bin Kiristi Yesu,
lino uNguluve ghwa lugudo nu lwa kukangasia amoojo avapele kuva nu vufumbue vwe vumo kwa muunhu ghweni kuling'ana nu Yesu Kilisite
6 don da zuciya ɗaya da kuma baki ɗaya kuke ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi.
awesie kuvomba ndiki kuvufumbue vumo muwesie kukumughinia mu njovele jino uNguluve nu Nhaata ghwa mwana ghwitu uYesu Kilisite.
7 Ta haka sai ku karɓi juna kamar yadda Kiristi ya karɓe ku, don a yabi Allah.
pe lino mumwupilaghe ghweni ndavule vule uKilisite alyavupile umue ku vwimike vwa Nguluve.
8 Ina dai gaya muku cewa Kiristi ya zama bawan Yahudawa a madadin gaskiyar Allah, don yă tabbatar da alkawaran da aka yi wa kakannin kakanninmu
ulwakuva nijova kuuti uKilisite avombilue kuva m'bombi ghwa kudumula igola ija m'bili ghwa kidimi kukwimila ilweki ja Nguluve. alyavombile ndiki kuuti ndeponu kuvonesia ulufingo luno lulyahumisivie ku vaNhaata,
9 domin Al’ummai su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa, kamar yadda yake a rubuce, “Saboda haka zan yabe ka a cikin Al’ummai; zan rera waƙoƙi ga sunanka.”
nava pa iisi kukumpaala uNguluve. ku vumosi vwake. ndavule vule jilembiluekuuti, “pe lino nihumia ulughinio kulyuve ku iisi simonga na kukwimba ulughinio kulitavua lyako.
10 Ya kuma ce, “Ku yi farin ciki, ya Al’ummai, tare da mutanensa.”
kange jiti, “kange hovokagha, umue mwe vaanhu va iisi, palikimo na vafue vake”.
11 Da kuma, “Ku yabi Ubangiji, dukanku Al’ummai, ku kuma rera masa yabo, dukanku mutanen duniya.”
kange, “mumughiniaghe uMutwa, mwe vanya iisi mweni; neka avaanhu ava iisi voni vamughiniaghe umwene”.
12 Kuma Ishaya ya ce, “Tushen Yesse zai tsiro, wanda zai taso yă yi mulkin al’ummai; al’ummai za su sa bege a gare shi.”
kange uYesayi akati, “kuliiva nu mhela ghwa Yese nu junge juno ilikwima kutema ku iisi sooni. avapanji viiva nuluhuvilo mwa mwene.
13 Bari Allah na bege yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama yayinda kuke dogara gare shi, domin ku yalwata cikin bege ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
lino uNguluve ghwa luhuvilo avamemesiaghe ulukelo lwoni nu lutengano lwa kwitika, neke kuuti ndeponu mughine ku luhuvilo ku ngufu sa Mhepo uMwimike.
14 Ni kaina na tabbata,’yan’uwana, cewa ku kanku kuna cike da kirki, cikakku cikin sani da kuma ƙwararru don yin wa juna gargaɗi.
vanyalukolo vango munidenginie, munidenginie kuuti najumue mumemilue uvugholofu, mdumemilue nu luhala lwoni. nidengilue kuuti, numue ndeponu mukangasianagha mweni.
15 Na rubuta muku gabagadi a kan waɗansu batuttuwa, don in sāke tuna muku su, saboda alherin da Allah ya ba ni
neke nikuvalembela kulukangasio kyongo mu simonga neke kukuvakumbusia kange, ulwakuva ikipeelua kino mupelilue nu Nguluve.
16 in zama mai hidimar Kiristi Yesu ga Al’ummai da aikin firist na yin shelar bisharar Allah, don Al’ummai su zama hadaya mai karɓuwa ga Allah, tsattsarka ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
ikipeelua iki kilyale kuuti ndeponu nive m'bombi ghwa Yesu kilisite juno alyasung'ilue mu iisi, kujihumia hwene ntemi ghwa livangili lya nguluve. nale niwesia kuvomba ndiki neke kujihumia kwango ku iisi kuve kwitikilue, kuvikilue patali nu Nguluve ku sila ja Mhepo uMwimike.
17 Saboda haka ina taƙama cikin Kiristi Yesu a cikin hidimata ga Allah.
pe ulukelo lwango luli mwa Kilisite yesu na mumbombo sa Nguluve.
18 Ba zan yi karambani in faɗi kome ba sai dai abin da Kiristi ya aikata ta wurina a jagorantar da Al’ummai su yi biyayya ga Allah ta wurin abin da na faɗa da kuma aikata
ulwakuva ndeponu naningaghele kujova lyolyoni looli kuuti uKilisite avombile kukilila kulyune uvwitiki vwa iisi. agha ghavombike ku masio na maghendele.
19 ta wurin ikon alamu da ayyukan banmamaki, da kuma ikon Ruhun Allah. Ta haka daga Urushalima har yă zuwa kewayen Illirikum, na yi wa’azin bisharar Kiristi.
ku ngufu sa fivalilo na gha kukwoghofia kwa ngufu sa Mhepo uMwimike. iji jilwale kuuti kuhuma ku Yelusalemu, na kusyutila kutali ndavule ku Ililiko, ndeponu kukujitola kunji ilivangili lwa Kilisite kuvunyilifu.
20 Labudda, burina shi ne in yi wa’azin bishara inda ba a san Kiristi ba, don kada yă zama ina gini ne a kan tushen da wani ya kafa.
ku sila iji, uvufumbue vwango vwale kupulisia ilivangili, neke na pepala pano uKilisite ikagulika ku litavua neke kuuti nikunuaghe kujenga uvwalo kwa muunhu ujunge.
21 Sai dai kamar yadda yake a rubuce, “Waɗanda ba a faɗa musu labarinsa ba za su gani, waɗanda kuma ba su ji ba za su fahimta.”
ndavule jilembilue kuuti, “vano kwa mwene vasila mhola sake angise mukumwagha, na vala vano navakampulike vilikunkagula”.
22 Wannan ne ya sa sau da yawa aka hana ni zuwa wurinku.
pe lino nikasighilue ke kinga kukwisa kulyumue,
23 Amma yanzu da babu sauran wurin da ya rage mini in yi aiki a waɗannan yankuna, da yake kuma shekaru masu yawa ina da marmari in gan ku,
neke lino nilinsila lubale lwolwoni mufighavo iifi kange nanogheluagha ku maka minga kukwisa kulyumue.
24 ina shirin yin haka in na tafi Sifen. Ina fata in ziyarce ku yayinda nake wucewa don ku raka ni can, bayan na ji daɗin zama tare da ku na ɗan lokaci.
lini jaatu ningakile pano niluta ku Hisipania nihuvila kuvavona. na kuwesia kutwalua ku sila jango palikimo numue, pe baho kyale nihovwike kuvomba lumo numue ku nsiki.
25 Yanzu kam, ina hanyata zuwa Urushalima don in kai gudummawa ga tsarkaka a can.
neke lino niluta ku Yelusalemu kukuvavombela avitiki avange.
26 Gama Makidoniya da Akayya sun ji daɗin yin gudummawa domin matalautan da suke cikin tsarkakan da suke a Urushalima.
ulwakuva lulyavanoghile avaanhu va kuMakedinia na ku Akaya kusangula isongo sino sinoghile ku avakotofu vamonga mu vitiki ku Yelusalemu.
27 Sun kuwa ji daɗin yin haka, gama ya zama kamar bashi ne a gare su. Da yake Al’ummai sun sami rabo cikin albarkun ruhaniyar Yahudawa, ya zama musu kamar bashi su ma su taimaki Yahudawa da albarkunsu na kayan duniya.
Ena, jilyale kulughano lwave, kange na ku kyang'haani valyale vasighilua vaave. lwakuva nave avapa iisi vahangilanile mu mbombo save isa mu mwoojo, voope kange visighilua kukuvavombela inofu ku vufumbue vwitu,
28 Saboda haka in na kammala wannan aiki na kuma tabbata cewa sun karɓi wannan amfani, zan tafi Sifen in kuma ziyarce ku a hanyata.
pe lino unsiki ghuno nivombile ndiki na kuva nulu kwilano lwa mheke iji kuveene, pe niluta mu sila palikimo numue ku Hisipania.
29 Na san cewa sa’ad da na zo wurinku, zan zo ne cikin yalwar albarkar Kiristi.
nikagula kuuti unsiki nikwisa kulyumue nikwisa ku vunywilifu vwa lufunyo lwa Kilisite.
30 Ina roƙonku’yan’uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma saboda ƙaunar Ruhu, ku haɗa kai tare da ni cikin famata ta wurin yin addu’a ga Allah saboda ni.
lino nikuvasuuma vanyalukolo kwa Mutwa ghwitu uYesu Kilisite na kulughano lwa Mhepo, kuuti muvombaghe palikimo nune mu nyifunyilo siinu ka Nguluve vwimila jango.
31 Ku yi addu’a don in kuɓuta daga hannun marasa bi a Yahudiya don kuma gudummawar da nake kaiwa Urushalima ta zama abar karɓa ga tsarkaka a can,
munisumilaghe kuuti ndeponu nipokua kuhuma kuva Yudea vano naviti. na kuuti imbombele jango ku Yelusalemu ndeponu jupiluaghe na vitiki.
32 don da yardar Allah, in iso wurinku da farin ciki in kuma wartsake tare da ku.
musuumilaghe kuuti ndeponu nikwisa kulyumue ku lukelo kukilila ulughano lwa Nguluve na kuuva ndeponu nipuma palikimo numue.
33 Allah na salama yă kasance tare da ku duka. Amin.
nu Nguluve ghwa lutengano avisaghe palikimo numue mweni. Ameni