< Romawa 15 >

1 Mu da muke da ƙarfi ya kamata mu yi haƙuri da kāsawar marasa ƙarfi ba kawai mu gamshi kanmu ba.
Now we who are strong ought to bear the weaknesses of the weak, and not to please ourselves.
2 Ya kamata kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai don kyautata zamansa domin kuma yă gina shi.
Let each one of us please his neighbor for that which is good, to be building him up.
3 Gama ko Kiristi ma bai gamshi kansa ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zage-zagen da waɗansu suka yi maka, duk sun fāɗo a kaina.”
For even Meshikha did not please himself. But, as it is written, "The insults of those who insult you fell on me."
4 Gama duk abin da aka rubuta a dā an rubuta ne domin yă koya mana, don ta wurin jimrewa da kuma ƙarfafawar Nassosi mu kasance da bege.
For whatever things were written before were written for our instruction, that through patience and through encouragement of the Scriptures we might have hope.
5 Bari Allah mai ba da haƙuri da kuma ƙarfafawa yă ba ku ruhun haɗinkai da juna yayinda kuke bin Kiristi Yesu,
Now the God of patience and of encouragement grant you to be of the same mind one with another according to Meshikha Yeshua,
6 don da zuciya ɗaya da kuma baki ɗaya kuke ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi.
that with one accord you may with one mouth glorify the God and Father of our Lord Yeshua Meshikha.
7 Ta haka sai ku karɓi juna kamar yadda Kiristi ya karɓe ku, don a yabi Allah.
Therefore accept one another, even as Meshikha also accepted you, to the glory of God.
8 Ina dai gaya muku cewa Kiristi ya zama bawan Yahudawa a madadin gaskiyar Allah, don yă tabbatar da alkawaran da aka yi wa kakannin kakanninmu
Now I say that Meshikha has been made a servant of the circumcision for the truth of God, that he might confirm the promises given to the fathers,
9 domin Al’ummai su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa, kamar yadda yake a rubuce, “Saboda haka zan yabe ka a cikin Al’ummai; zan rera waƙoƙi ga sunanka.”
and that the non-Jews might glorify God for his mercy. As it is written, "therefore I will give praise to you among the non-Jews, and sing to your name."
10 Ya kuma ce, “Ku yi farin ciki, ya Al’ummai, tare da mutanensa.”
Again he says, "Rejoice, you nations, with his people."
11 Da kuma, “Ku yabi Ubangiji, dukanku Al’ummai, ku kuma rera masa yabo, dukanku mutanen duniya.”
Again, "Praise the Lord, all you nations. Let all the peoples praise him."
12 Kuma Ishaya ya ce, “Tushen Yesse zai tsiro, wanda zai taso yă yi mulkin al’ummai; al’ummai za su sa bege a gare shi.”
Again, Eshaya says, "There will be the root of Ishai, he who arises to rule over the peoples; in him will the nations hope."
13 Bari Allah na bege yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama yayinda kuke dogara gare shi, domin ku yalwata cikin bege ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
Now may the God of hope fill you with all joy and peace in believing, that you may abound in hope, in the power of the Rukha d'Qudsha.
14 Ni kaina na tabbata,’yan’uwana, cewa ku kanku kuna cike da kirki, cikakku cikin sani da kuma ƙwararru don yin wa juna gargaɗi.
I myself am also persuaded about you, my brothers, that you yourselves are full of goodness, filled with all knowledge, able also to admonish others.
15 Na rubuta muku gabagadi a kan waɗansu batuttuwa, don in sāke tuna muku su, saboda alherin da Allah ya ba ni
But I write the more boldly to you in part, as reminding you, because of the grace that was given to me by God,
16 in zama mai hidimar Kiristi Yesu ga Al’ummai da aikin firist na yin shelar bisharar Allah, don Al’ummai su zama hadaya mai karɓuwa ga Allah, tsattsarka ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
that I should be a servant of Meshikha Yeshua to the non-Jews, serving as a priest the Good News of God, that the offering up of the non-Jews might be made acceptable, sanctified by the Rukha d'Qudsha.
17 Saboda haka ina taƙama cikin Kiristi Yesu a cikin hidimata ga Allah.
I have therefore my boasting in Meshikha Yeshua in things pertaining to God.
18 Ba zan yi karambani in faɗi kome ba sai dai abin da Kiristi ya aikata ta wurina a jagorantar da Al’ummai su yi biyayya ga Allah ta wurin abin da na faɗa da kuma aikata
For I will not dare to speak of any things except those which Meshikha worked through me, for the obedience of the non-Jews, by word and deed,
19 ta wurin ikon alamu da ayyukan banmamaki, da kuma ikon Ruhun Allah. Ta haka daga Urushalima har yă zuwa kewayen Illirikum, na yi wa’azin bisharar Kiristi.
in the power of signs and wonders, in the power of the Rukha of God; so that from Urishlim, and around as far as to Illyricum, I have fully preached the Good News of Meshikha.
20 Labudda, burina shi ne in yi wa’azin bishara inda ba a san Kiristi ba, don kada yă zama ina gini ne a kan tushen da wani ya kafa.
And in this way I desire to preach the Good News where Meshikha was not known, that I might not build on another's foundation.
21 Sai dai kamar yadda yake a rubuce, “Waɗanda ba a faɗa musu labarinsa ba za su gani, waɗanda kuma ba su ji ba za su fahimta.”
But, as it is written, "Those who were not told about him, they will see, and those who have not heard, they will understand."
22 Wannan ne ya sa sau da yawa aka hana ni zuwa wurinku.
Therefore also I was hindered these many times from coming to you,
23 Amma yanzu da babu sauran wurin da ya rage mini in yi aiki a waɗannan yankuna, da yake kuma shekaru masu yawa ina da marmari in gan ku,
but now, no longer having any place in these regions, and having these many years a longing to come to you,
24 ina shirin yin haka in na tafi Sifen. Ina fata in ziyarce ku yayinda nake wucewa don ku raka ni can, bayan na ji daɗin zama tare da ku na ɗan lokaci.
whenever I journey to Spain I will come to you. For I hope to see you on my journey, and to be helped on my way there by you, if first I may enjoy your company for a while.
25 Yanzu kam, ina hanyata zuwa Urushalima don in kai gudummawa ga tsarkaka a can.
But now, I say, I am going to Urishlim, serving the saints.
26 Gama Makidoniya da Akayya sun ji daɗin yin gudummawa domin matalautan da suke cikin tsarkakan da suke a Urushalima.
For it has been the good pleasure of Macedonia and Achaia to make a certain contribution for the poor among the saints who are at Urishlim.
27 Sun kuwa ji daɗin yin haka, gama ya zama kamar bashi ne a gare su. Da yake Al’ummai sun sami rabo cikin albarkun ruhaniyar Yahudawa, ya zama musu kamar bashi su ma su taimaki Yahudawa da albarkunsu na kayan duniya.
Yes, it has been their good pleasure, and they are their debtors. For if the non-Jewish people have been made partakers of their spiritual things, they owe it to them also to serve them in fleshly things.
28 Saboda haka in na kammala wannan aiki na kuma tabbata cewa sun karɓi wannan amfani, zan tafi Sifen in kuma ziyarce ku a hanyata.
When therefore I have accomplished this, and have sealed to them this fruit, I will go on by way of you to Spain.
29 Na san cewa sa’ad da na zo wurinku, zan zo ne cikin yalwar albarkar Kiristi.
I know that, when I come to you, I will come in the fullness of the blessing of Meshikha.
30 Ina roƙonku’yan’uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma saboda ƙaunar Ruhu, ku haɗa kai tare da ni cikin famata ta wurin yin addu’a ga Allah saboda ni.
Now I appeal to you, brothers, by our Lord Yeshua Meshikha, and by the love of the Rukha, that you strive together with me in your prayers to God for me,
31 Ku yi addu’a don in kuɓuta daga hannun marasa bi a Yahudiya don kuma gudummawar da nake kaiwa Urushalima ta zama abar karɓa ga tsarkaka a can,
that I may be delivered from those who are disobedient in Yehuda, and that my service which I have for Urishlim may be acceptable to the saints;
32 don da yardar Allah, in iso wurinku da farin ciki in kuma wartsake tare da ku.
that I may come to you in joy through the will of God, and together with you, find rest.
33 Allah na salama yă kasance tare da ku duka. Amin.
Now the God of peace be with you all. Amen.

< Romawa 15 >