< Romawa 15 >

1 Mu da muke da ƙarfi ya kamata mu yi haƙuri da kāsawar marasa ƙarfi ba kawai mu gamshi kanmu ba.
And we ought—we who are strong—to bear the weaknesses of the powerless, and not to please ourselves;
2 Ya kamata kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai don kyautata zamansa domin kuma yă gina shi.
for let each one of us please the neighbor for good, for edification,
3 Gama ko Kiristi ma bai gamshi kansa ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zage-zagen da waɗansu suka yi maka, duk sun fāɗo a kaina.”
for even the Christ did not please Himself, but according as it has been written: “The reproaches of those reproaching You fell on Me”;
4 Gama duk abin da aka rubuta a dā an rubuta ne domin yă koya mana, don ta wurin jimrewa da kuma ƙarfafawar Nassosi mu kasance da bege.
for as many things as were written before, for our instruction were written before, that through the endurance, and the exhortation of the Writings, we might have the hope.
5 Bari Allah mai ba da haƙuri da kuma ƙarfafawa yă ba ku ruhun haɗinkai da juna yayinda kuke bin Kiristi Yesu,
And may the God of the endurance, and of the exhortation, give to you to have the same mind toward one another, according to Christ Jesus,
6 don da zuciya ɗaya da kuma baki ɗaya kuke ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi.
that with one accord—with one mouth—you may glorify the God and Father of our Lord Jesus Christ;
7 Ta haka sai ku karɓi juna kamar yadda Kiristi ya karɓe ku, don a yabi Allah.
for this reason receive one another, according as also the Christ received us, to the glory of God.
8 Ina dai gaya muku cewa Kiristi ya zama bawan Yahudawa a madadin gaskiyar Allah, don yă tabbatar da alkawaran da aka yi wa kakannin kakanninmu
And I say Jesus Christ to have become a servant of circumcision for the truth of God, to confirm the promises to the fathers,
9 domin Al’ummai su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa, kamar yadda yake a rubuce, “Saboda haka zan yabe ka a cikin Al’ummai; zan rera waƙoƙi ga sunanka.”
and the nations for kindness to glorify God, according as it has been written: “Because of this I will confess to You among nations, and to Your Name I will sing praise”;
10 Ya kuma ce, “Ku yi farin ciki, ya Al’ummai, tare da mutanensa.”
and again it says, “Rejoice you nations, with His people”;
11 Da kuma, “Ku yabi Ubangiji, dukanku Al’ummai, ku kuma rera masa yabo, dukanku mutanen duniya.”
and again, “Praise the LORD, all you nations; and laud Him, all you peoples”;
12 Kuma Ishaya ya ce, “Tushen Yesse zai tsiro, wanda zai taso yă yi mulkin al’ummai; al’ummai za su sa bege a gare shi.”
and again, Isaiah says, “There will be the root of Jesse, and He who is rising to rule nations—on Him will nations hope”;
13 Bari Allah na bege yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama yayinda kuke dogara gare shi, domin ku yalwata cikin bege ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
and the God of the hope will fill you with all joy and peace in the believing, for your abounding in the hope in power of the Holy Spirit.
14 Ni kaina na tabbata,’yan’uwana, cewa ku kanku kuna cike da kirki, cikakku cikin sani da kuma ƙwararru don yin wa juna gargaɗi.
And I am persuaded, my brothers—I myself also—concerning you, that you yourselves also are full of goodness, having been filled with all knowledge, also able to admonish one another;
15 Na rubuta muku gabagadi a kan waɗansu batuttuwa, don in sāke tuna muku su, saboda alherin da Allah ya ba ni
and the more boldly I wrote to you, brothers, in part, as putting you in mind, because of the grace that is given to me by God,
16 in zama mai hidimar Kiristi Yesu ga Al’ummai da aikin firist na yin shelar bisharar Allah, don Al’ummai su zama hadaya mai karɓuwa ga Allah, tsattsarka ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
for my being a servant of Jesus Christ to the nations, acting as priest in the good news of God, that the offering up of the nations may become acceptable, sanctified by the Holy Spirit.
17 Saboda haka ina taƙama cikin Kiristi Yesu a cikin hidimata ga Allah.
I have, then, a boasting in Christ Jesus, in the things pertaining to God,
18 Ba zan yi karambani in faɗi kome ba sai dai abin da Kiristi ya aikata ta wurina a jagorantar da Al’ummai su yi biyayya ga Allah ta wurin abin da na faɗa da kuma aikata
for I will not dare to speak anything of the things that Christ did not work through me, to obedience of nations, by word and deed,
19 ta wurin ikon alamu da ayyukan banmamaki, da kuma ikon Ruhun Allah. Ta haka daga Urushalima har yă zuwa kewayen Illirikum, na yi wa’azin bisharar Kiristi.
in power of signs and wonders, in power of the Spirit of God; so that I, from Jerusalem, and in a circle as far as Illyricum, have fully preached the good news of the Christ;
20 Labudda, burina shi ne in yi wa’azin bishara inda ba a san Kiristi ba, don kada yă zama ina gini ne a kan tushen da wani ya kafa.
and so counting it honor to proclaim good news, not where Christ was named—that on another’s foundation I might not build—
21 Sai dai kamar yadda yake a rubuce, “Waɗanda ba a faɗa musu labarinsa ba za su gani, waɗanda kuma ba su ji ba za su fahimta.”
but according as it has been written: “To whom it was not told concerning Him, they will see; and they who have not heard, will understand.”
22 Wannan ne ya sa sau da yawa aka hana ni zuwa wurinku.
For this reason, also, I was hindered many times from coming to you,
23 Amma yanzu da babu sauran wurin da ya rage mini in yi aiki a waɗannan yankuna, da yake kuma shekaru masu yawa ina da marmari in gan ku,
and now, no longer having place in these parts, and having a longing to come to you for many years,
24 ina shirin yin haka in na tafi Sifen. Ina fata in ziyarce ku yayinda nake wucewa don ku raka ni can, bayan na ji daɗin zama tare da ku na ɗan lokaci.
when I may go on to Spain I will come to you, for I hope in going through, to see you, and by you to be set forward there, if of you first, in part, I will be filled.
25 Yanzu kam, ina hanyata zuwa Urushalima don in kai gudummawa ga tsarkaka a can.
And now, I go on to Jerusalem, ministering to the holy ones;
26 Gama Makidoniya da Akayya sun ji daɗin yin gudummawa domin matalautan da suke cikin tsarkakan da suke a Urushalima.
for it pleased Macedonia and Achaia well to make a certain contribution for the poor of the holy ones who [are] in Jerusalem;
27 Sun kuwa ji daɗin yin haka, gama ya zama kamar bashi ne a gare su. Da yake Al’ummai sun sami rabo cikin albarkun ruhaniyar Yahudawa, ya zama musu kamar bashi su ma su taimaki Yahudawa da albarkunsu na kayan duniya.
for it pleased well, and their debtors they are, for if the nations participated in their spiritual things, they ought also, in the fleshly things, to minister to them.
28 Saboda haka in na kammala wannan aiki na kuma tabbata cewa sun karɓi wannan amfani, zan tafi Sifen in kuma ziyarce ku a hanyata.
This, then, having finished, and having sealed to them this fruit, I will return through you, to Spain;
29 Na san cewa sa’ad da na zo wurinku, zan zo ne cikin yalwar albarkar Kiristi.
and I have known that coming to you—in the fullness of the blessing of the good news of Christ I will come.
30 Ina roƙonku’yan’uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma saboda ƙaunar Ruhu, ku haɗa kai tare da ni cikin famata ta wurin yin addu’a ga Allah saboda ni.
And I call on you, brothers, through our Lord Jesus Christ, and through the love of the Spirit, to strive together with me in the prayers for me to God,
31 Ku yi addu’a don in kuɓuta daga hannun marasa bi a Yahudiya don kuma gudummawar da nake kaiwa Urushalima ta zama abar karɓa ga tsarkaka a can,
that I may be delivered from those not believing in Judea, and that my ministry, that [is] for Jerusalem, may become acceptable to the holy ones;
32 don da yardar Allah, in iso wurinku da farin ciki in kuma wartsake tare da ku.
that in joy I may come to you, through the will of God, and may be refreshed with you,
33 Allah na salama yă kasance tare da ku duka. Amin.
and the God of peace [be] with you all. Amen.

< Romawa 15 >