< Romawa 15 >

1 Mu da muke da ƙarfi ya kamata mu yi haƙuri da kāsawar marasa ƙarfi ba kawai mu gamshi kanmu ba.
But we who are stronger must bear with the feebleness of the weak, and not so as to please ourselves.
2 Ya kamata kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai don kyautata zamansa domin kuma yă gina shi.
Each one of you should please his neighbor unto good, for edification.
3 Gama ko Kiristi ma bai gamshi kansa ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zage-zagen da waɗansu suka yi maka, duk sun fāɗo a kaina.”
For even Christ did not please himself, but as it was written: “The reproaches of those who reproached you fell upon me.”
4 Gama duk abin da aka rubuta a dā an rubuta ne domin yă koya mana, don ta wurin jimrewa da kuma ƙarfafawar Nassosi mu kasance da bege.
For whatever was written, was written to teach us, so that, through patience and the consolation of the Scriptures, we might have hope.
5 Bari Allah mai ba da haƙuri da kuma ƙarfafawa yă ba ku ruhun haɗinkai da juna yayinda kuke bin Kiristi Yesu,
So may the God of patience and solace grant you to be of one mind toward one another, in accord with Jesus Christ,
6 don da zuciya ɗaya da kuma baki ɗaya kuke ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi.
so that, together with one mouth, you may glorify the God and Father of our Lord Jesus Christ.
7 Ta haka sai ku karɓi juna kamar yadda Kiristi ya karɓe ku, don a yabi Allah.
For this reason, accept one another, just as Christ also has accepted you, in the honor of God.
8 Ina dai gaya muku cewa Kiristi ya zama bawan Yahudawa a madadin gaskiyar Allah, don yă tabbatar da alkawaran da aka yi wa kakannin kakanninmu
For I declare that Christ Jesus was the minister of circumcision because of the truth of God, so as to confirm the promises to the fathers,
9 domin Al’ummai su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa, kamar yadda yake a rubuce, “Saboda haka zan yabe ka a cikin Al’ummai; zan rera waƙoƙi ga sunanka.”
and that the Gentiles are to honor God because of his mercy, just as it was written: “Because of this, I will confess you among the Gentiles, O Lord, and I will sing to your name.”
10 Ya kuma ce, “Ku yi farin ciki, ya Al’ummai, tare da mutanensa.”
And again, he says: “Rejoice, O Gentiles, along with his people.”
11 Da kuma, “Ku yabi Ubangiji, dukanku Al’ummai, ku kuma rera masa yabo, dukanku mutanen duniya.”
And again: “All Gentiles, praise the Lord; and all peoples, magnify him.”
12 Kuma Ishaya ya ce, “Tushen Yesse zai tsiro, wanda zai taso yă yi mulkin al’ummai; al’ummai za su sa bege a gare shi.”
And again, Isaiah says: “There shall be a root of Jesse, and he shall rise up to rule the Gentiles, and in him the Gentiles shall hope.”
13 Bari Allah na bege yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama yayinda kuke dogara gare shi, domin ku yalwata cikin bege ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
So may the God of hope fill you with every joy and with peace in believing, so that you may abound in hope and in the virtue of the Holy Spirit.
14 Ni kaina na tabbata,’yan’uwana, cewa ku kanku kuna cike da kirki, cikakku cikin sani da kuma ƙwararru don yin wa juna gargaɗi.
But I am also certain about you, my brothers, that you also have been filled with love, completed with all knowledge, so that you are able to admonish one another.
15 Na rubuta muku gabagadi a kan waɗansu batuttuwa, don in sāke tuna muku su, saboda alherin da Allah ya ba ni
But I have written to you, brothers, more boldly than to the others, as if calling you to mind again, because of the grace which has been given to me from God,
16 in zama mai hidimar Kiristi Yesu ga Al’ummai da aikin firist na yin shelar bisharar Allah, don Al’ummai su zama hadaya mai karɓuwa ga Allah, tsattsarka ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
so that I may be a minister of Christ Jesus among the Gentiles, sanctifying the Gospel of God, in order that the oblation of the Gentiles may be made acceptable and may be sanctified in the Holy Spirit.
17 Saboda haka ina taƙama cikin Kiristi Yesu a cikin hidimata ga Allah.
Therefore, I have glory in Christ Jesus before God.
18 Ba zan yi karambani in faɗi kome ba sai dai abin da Kiristi ya aikata ta wurina a jagorantar da Al’ummai su yi biyayya ga Allah ta wurin abin da na faɗa da kuma aikata
So I dare not speak of any of those things which Christ does not effect through me, unto the obedience of the Gentiles, in word and deed,
19 ta wurin ikon alamu da ayyukan banmamaki, da kuma ikon Ruhun Allah. Ta haka daga Urushalima har yă zuwa kewayen Illirikum, na yi wa’azin bisharar Kiristi.
with the power of signs and wonders, by power of the Holy Spirit. For in this way, from Jerusalem, throughout its surroundings, as far as Illyricum, I have replenished the Gospel of Christ.
20 Labudda, burina shi ne in yi wa’azin bishara inda ba a san Kiristi ba, don kada yă zama ina gini ne a kan tushen da wani ya kafa.
And so I have preached this Gospel, not where Christ was known by name, lest I build upon the foundation of another,
21 Sai dai kamar yadda yake a rubuce, “Waɗanda ba a faɗa musu labarinsa ba za su gani, waɗanda kuma ba su ji ba za su fahimta.”
but just as it was written: “Those to whom he was not announced shall perceive, and those who have not heard shall understand.”
22 Wannan ne ya sa sau da yawa aka hana ni zuwa wurinku.
Because of this also, I was greatly hindered in coming to you, and I have been prevented until the present time.
23 Amma yanzu da babu sauran wurin da ya rage mini in yi aiki a waɗannan yankuna, da yake kuma shekaru masu yawa ina da marmari in gan ku,
Yet truly now, having no other destination in these regions, and having already had a great desire to come to you over the past many years,
24 ina shirin yin haka in na tafi Sifen. Ina fata in ziyarce ku yayinda nake wucewa don ku raka ni can, bayan na ji daɗin zama tare da ku na ɗan lokaci.
when I begin to set out on my journey to Spain, I hope that, as I pass by, I may see you, and I may be guided from there by you, after first having borne some fruit among you.
25 Yanzu kam, ina hanyata zuwa Urushalima don in kai gudummawa ga tsarkaka a can.
But next I will set out for Jerusalem, to minister to the saints.
26 Gama Makidoniya da Akayya sun ji daɗin yin gudummawa domin matalautan da suke cikin tsarkakan da suke a Urushalima.
For those of Macedonia and Achaia have decided to make a collection for those of the poor among the saints who are at Jerusalem.
27 Sun kuwa ji daɗin yin haka, gama ya zama kamar bashi ne a gare su. Da yake Al’ummai sun sami rabo cikin albarkun ruhaniyar Yahudawa, ya zama musu kamar bashi su ma su taimaki Yahudawa da albarkunsu na kayan duniya.
And this has pleased them, because they are in their debt. For, since the Gentiles have become partakers of their spiritual things, they also ought to minister to them in worldly things.
28 Saboda haka in na kammala wannan aiki na kuma tabbata cewa sun karɓi wannan amfani, zan tafi Sifen in kuma ziyarce ku a hanyata.
Therefore, when I have completed this task, and have consigned to them this fruit, I shall set out, by way of you, to Spain.
29 Na san cewa sa’ad da na zo wurinku, zan zo ne cikin yalwar albarkar Kiristi.
And I know that when I come to you I shall arrive with an abundance of the blessings of the Gospel of Christ.
30 Ina roƙonku’yan’uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma saboda ƙaunar Ruhu, ku haɗa kai tare da ni cikin famata ta wurin yin addu’a ga Allah saboda ni.
Therefore, I beg you, brothers, through our Lord Jesus Christ and through the love of the Holy Spirit, that you assist me with your prayers to God on my behalf,
31 Ku yi addu’a don in kuɓuta daga hannun marasa bi a Yahudiya don kuma gudummawar da nake kaiwa Urushalima ta zama abar karɓa ga tsarkaka a can,
so that I may be freed from the unfaithful who are in Judea, and so that the oblation of my service may be acceptable to the saints in Jerusalem.
32 don da yardar Allah, in iso wurinku da farin ciki in kuma wartsake tare da ku.
So may I come to you with joy, through the will of God, and so may I be refreshed with you.
33 Allah na salama yă kasance tare da ku duka. Amin.
And may the God of peace be with you all. Amen.

< Romawa 15 >