< Romawa 15 >

1 Mu da muke da ƙarfi ya kamata mu yi haƙuri da kāsawar marasa ƙarfi ba kawai mu gamshi kanmu ba.
Men vi, som ere stærke, bør bære de svages Skrøbeligheder og ikke være os selv til Behag.
2 Ya kamata kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai don kyautata zamansa domin kuma yă gina shi.
Enhver af os være sin Næste til Behag til det gode, til Opbyggelse.
3 Gama ko Kiristi ma bai gamshi kansa ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zage-zagen da waɗansu suka yi maka, duk sun fāɗo a kaina.”
Thi også Kristus var ikke sig selv til Behag; men, som der er skrevet: "Deres Forhånelser, som håne dig, ere faldne på mig."
4 Gama duk abin da aka rubuta a dā an rubuta ne domin yă koya mana, don ta wurin jimrewa da kuma ƙarfafawar Nassosi mu kasance da bege.
Thi alt, hvad der er skrevet tilforn, det er skrevet til vor Belæring, for at vi skulle have Håbet ved Udholdenheden og Skrifternes Trøst.
5 Bari Allah mai ba da haƙuri da kuma ƙarfafawa yă ba ku ruhun haɗinkai da juna yayinda kuke bin Kiristi Yesu,
Men Udholdenhedensog Trøstens Gud give eder at være enige indbyrdes, som Kristus Jesus vil det,
6 don da zuciya ɗaya da kuma baki ɗaya kuke ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi.
for at I endrægtigt med een Mund kunne prise Gud og vor Herres Jesu Kristi Fader.
7 Ta haka sai ku karɓi juna kamar yadda Kiristi ya karɓe ku, don a yabi Allah.
Derfor tager eder af hverandre, ligesom også Kristus har taget sig af os, til Guds Ære.
8 Ina dai gaya muku cewa Kiristi ya zama bawan Yahudawa a madadin gaskiyar Allah, don yă tabbatar da alkawaran da aka yi wa kakannin kakanninmu
Jeg siger nemlig, at Kristus er bleven Tjener for omskårne for Guds Sanddruheds Skyld for at stadfæste Forjættelserne til Fædrene;
9 domin Al’ummai su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa, kamar yadda yake a rubuce, “Saboda haka zan yabe ka a cikin Al’ummai; zan rera waƙoƙi ga sunanka.”
men at Hedningerne skulle prise Gud for hans Barmhjertigheds Skyld, som der er skrevet: "Derfor vil jeg bekende dig iblandt Hedninger og lovsynge dit Navn,"
10 Ya kuma ce, “Ku yi farin ciki, ya Al’ummai, tare da mutanensa.”
Og atter siges der: "Fryder eder, I Hedninger, med hans Folk!"
11 Da kuma, “Ku yabi Ubangiji, dukanku Al’ummai, ku kuma rera masa yabo, dukanku mutanen duniya.”
Og atter: "Lover Herren, alle Hedninger, og alle Folkene skulle prise ham."
12 Kuma Ishaya ya ce, “Tushen Yesse zai tsiro, wanda zai taso yă yi mulkin al’ummai; al’ummai za su sa bege a gare shi.”
Og atter siger Esajas: "Komme skal Isajs Rodskud og han, der rejser sig for at herske over Hedninger; på ham skulle Hedninger håbe."
13 Bari Allah na bege yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama yayinda kuke dogara gare shi, domin ku yalwata cikin bege ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.
Men Håbets Gud fylde eder med al Glæde og Fred, idet I tro, for at I må blive rige i Håbet ved den Helligånds Kraft!
14 Ni kaina na tabbata,’yan’uwana, cewa ku kanku kuna cike da kirki, cikakku cikin sani da kuma ƙwararru don yin wa juna gargaɗi.
Men også jeg, mine Brødre! har selv den Forvisning om eder, at I også selv ere fulde af Godhed, fyldte med al Kundskab, i Stand til også at påminde hverandre.
15 Na rubuta muku gabagadi a kan waɗansu batuttuwa, don in sāke tuna muku su, saboda alherin da Allah ya ba ni
Dog har jeg for en Del tilskrevet eder noget dristigere for at påminde eder på Grund af den Nåde, som er given mig fra Gud
16 in zama mai hidimar Kiristi Yesu ga Al’ummai da aikin firist na yin shelar bisharar Allah, don Al’ummai su zama hadaya mai karɓuwa ga Allah, tsattsarka ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
til iblandt Hedningerne at være en Kristi Jesu Offertjener, der som Præst betjener Guds Evangelium, for at Hedningerne må blive et velbehageligt Offer, helliget ved den Helligånd.
17 Saboda haka ina taƙama cikin Kiristi Yesu a cikin hidimata ga Allah.
Således har jeg min Ros i Kristus Jesus af min Tjeneste for Gud.
18 Ba zan yi karambani in faɗi kome ba sai dai abin da Kiristi ya aikata ta wurina a jagorantar da Al’ummai su yi biyayya ga Allah ta wurin abin da na faɗa da kuma aikata
Thi jeg vil ikke driste mig til at tale om noget af det, som Kristus ikke har udført ved mig til at virke Hedningers Lydighed, ved Ord og Handling,
19 ta wurin ikon alamu da ayyukan banmamaki, da kuma ikon Ruhun Allah. Ta haka daga Urushalima har yă zuwa kewayen Illirikum, na yi wa’azin bisharar Kiristi.
ved Tegns og Undergerningers Kraft, ved Guds Ånds Kraft, så at jeg fra Jerusalem og trindt omkring indtil Illyrien har til fulde forkyndt Kristi Evangelium;
20 Labudda, burina shi ne in yi wa’azin bishara inda ba a san Kiristi ba, don kada yă zama ina gini ne a kan tushen da wani ya kafa.
dog således, at jeg sætter min Ære i at forkynde Evangeliet ikke der, hvor Kristus er nævnet, for at jeg, ikke skal bygge på en andens Grundvold,
21 Sai dai kamar yadda yake a rubuce, “Waɗanda ba a faɗa musu labarinsa ba za su gani, waɗanda kuma ba su ji ba za su fahimta.”
men, som der er skrevet: "De, for hvem der ikke blev kundgjort om ham, skulle se, og de, som ikke have hørt, skulle forstå."
22 Wannan ne ya sa sau da yawa aka hana ni zuwa wurinku.
Derfor er jeg også de mange Gange bleven forhindret i at komme til eder.
23 Amma yanzu da babu sauran wurin da ya rage mini in yi aiki a waɗannan yankuna, da yake kuma shekaru masu yawa ina da marmari in gan ku,
Men nu, da jeg ikke mere har Rum i disse Egne og i mange År har haft Længsel efter at komme til eder,
24 ina shirin yin haka in na tafi Sifen. Ina fata in ziyarce ku yayinda nake wucewa don ku raka ni can, bayan na ji daɗin zama tare da ku na ɗan lokaci.
vil jeg, når jeg rejser til Spanien, komme til eder; thi jeg håber at se eder på Gennemrejsen og af eder at blive befordret derhen, når jeg først i nogen Måde er bleven tilfredsstillet hos eder.
25 Yanzu kam, ina hanyata zuwa Urushalima don in kai gudummawa ga tsarkaka a can.
Men nu rejser jeg til Jerusalem i Tjeneste for de hellige.
26 Gama Makidoniya da Akayya sun ji daɗin yin gudummawa domin matalautan da suke cikin tsarkakan da suke a Urushalima.
Thi Makedonien og Akaja have fundet Glæde i at gøre et Sammenskud til de fattige iblandt de hellige i Jerusalem.
27 Sun kuwa ji daɗin yin haka, gama ya zama kamar bashi ne a gare su. Da yake Al’ummai sun sami rabo cikin albarkun ruhaniyar Yahudawa, ya zama musu kamar bashi su ma su taimaki Yahudawa da albarkunsu na kayan duniya.
De have nemlig fundet Glæde deri, og de ere deres Skyldnere. Thi ere Hedningerne blevne delagtige i hines åndelige Goder, da ere de også skyldige at tjene dem med de timelige.
28 Saboda haka in na kammala wannan aiki na kuma tabbata cewa sun karɓi wannan amfani, zan tafi Sifen in kuma ziyarce ku a hanyata.
Når jeg da har fuldbragt dette og beseglet denne Frugt for dem, vil jeg derfra drage om ad eder til Spanien.
29 Na san cewa sa’ad da na zo wurinku, zan zo ne cikin yalwar albarkar Kiristi.
Men jeg ved, at når jeg kommer til eder, skal jeg komme med Kristi Velsignelses Fylde.
30 Ina roƙonku’yan’uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma saboda ƙaunar Ruhu, ku haɗa kai tare da ni cikin famata ta wurin yin addu’a ga Allah saboda ni.
Men jeg formaner eder, Brødre! ved vor Herre Jesus Kristus og ved Åndens Kærlighed til med mig at stride i eders Bønner for mig til Gud,
31 Ku yi addu’a don in kuɓuta daga hannun marasa bi a Yahudiya don kuma gudummawar da nake kaiwa Urushalima ta zama abar karɓa ga tsarkaka a can,
for at jeg må udfries fra de genstridige i Judæa, og mit Ærinde til Jerusalem må blive de hellige kærkomment,
32 don da yardar Allah, in iso wurinku da farin ciki in kuma wartsake tare da ku.
for at jeg kan komme til eder med Glæde, ved Guds Villie, og vederkvæges med eder.
33 Allah na salama yă kasance tare da ku duka. Amin.
Men Fredens Gud være med eder alle! Amen.

< Romawa 15 >