< Romawa 14 >
1 Ku karɓi wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, amma fa kada ku hukunta shi a kan abubuwan da ake da shakka a kai ba.
To him who is feeble in the faith, reach forth the hand. And be not divided in your thoughts.
2 Bangaskiyar mutum ta yarda masa yă ci kome, amma wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, yakan ci kayan lambu ne kawai.
For one man believeth, that he may eat every thing: and he that is feeble, eateth herbs.
3 Mutumin da yake cin kowane irin abinci, kada yă rena wanda ba ya cin, wanda kuma ba ya cin kowane irin abinci, kada yă ga laifin mutumin da yake ci, domin Allah ya riga ya karɓe shi.
And he that eateth, should not despise him that eateth not; and he that eateth not, should not judge him that eateth, for God hath received him.
4 Kai wane ne har da za ka ga laifin bawan wani? Ko bawan yă yi aiki mai kyau, ko yă kāsa, ai, wannan ruwan maigidansa ne. Za a ma tsai da shi, domin Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
Who art thou, that thou judgest a servant not thine; and who, if he standeth, he standeth to his Lord; and if he falleth, he falleth to his Lord? But he will assuredly stand; for his Lord hath power to establish him.
5 Wani yakan ɗauki wata rana da daraja fiye da sauran ranaku; wani kuma yana ganin dukan ranakun ɗaya ne. Ya kamata kowa yă kasance da tabbaci a cikin zuciyarsa.
One man discriminateth between days; and another judgeth all days alike. But let every one be sure, in regard to his knowledge.
6 Wannan mai ɗaukan rana ɗaya da muhimmanci fiye da sauran, yana yin haka ne ga Ubangiji. Wannan mai cin nama, yana yin haka ne ga Ubangiji, gama yakan yi godiya ga Allah; wannan da ba ya ci kuwa, yana yin haka ne ga Ubangiji yana kuwa yin godiya ga Allah.
He that esteemeth a day, esteemeth it for his Lord: and he that esteemeth not a day, for his Lord, he doth not esteem it. And he that eateth, eateth to his Lord, and giveth thanks to God: and he that eateth not, to his Lord he eateth not, and giveth thanks to God.
7 Gama ba waninmu da yake rayuwa wa kansa kaɗai, kuma ba waninmu da kan mutu don kansa kaɗai.
For there is not one of us, who liveth for himself: and there is not one, who dieth for himself.
8 In muna rayuwa, muna rayuwa ne ga Ubangiji; in kuma muna mutuwa, muna mutuwa ne ga Ubangiji. Saboda haka, ko muna a raye ko muna a mace, mu na Ubangiji ne.
Because, if we live, to our Lord it is we live; or if we die, to our Lord it is we die. Whether we live, therefore, or whether we die, we are our Lord's.
9 Saboda wannan ne Kiristi ya mutu, ya kuma sāke rayuwa domin yă zama Ubangiji na matattu da na masu rai.
Moreover, for this cause Messiah died, and revived, and arose; that he might be Lord of the dead and of the living.
10 Kai kuwa, don me kake ganin laifin ɗan’uwanka? Ko kuma don me kake rena ɗan’uwanka? Gama duk za mu tsaya a gaban kujerar shari’ar Allah.
But thou, why dost thou judge thy brother? or, why dost thou despise thy brother? For we must all stand before the judgment seat of Messiah,
11 A rubuce yake cewa, “‘Muddin ina raye,’ in ji Ubangiji, ‘kowace gwiwa za tă durƙusa a gabana; kowane harshe kuma zai furta wa Allah.’”
as it is written: As I live, saith the Lord, to me every knee shall bow; and to me every tongue shall give praise.
12 Don haka kowannenmu zai ba da lissafin kansa ga Allah.
So then, every one of us must give account of himself to God.
13 Saboda haka bari mu daina ba wa juna laifi. A maimakon, sai kowa yă yi niyya ba zai sa dutsen tuntuɓe ko abin sa fāɗuwa a hanyar ɗan’uwansa ba.
Henceforth, judge ye not one another; but rather, judge ye this, that thou erect not a stumbling-block for thy brother.
14 A matsayina na mai bin Ubangiji Yesu na tabbata ƙwarai cewa babu abincin da yake marar tsabta don kansa. Amma in wani ya ɗauka wani abu marar tsabta ne, to, a gare shi marar tsabta ne.
I know indeed, and am persuaded by the Lord Jesus, that there is nothing which is unclean in itself; but to him who thinketh any thing to be unclean, to him only it is defiled.
15 In kana ɓata wa ɗan’uwanka zuciya saboda abincin da kake ci, ba halin ƙauna kake nunawa ba ke nan. Kada abincin da kake ci yă zama hanyar lalatar da ɗan’uwanka wanda Kiristi ya mutu dominsa.
But if thou grievest thy brother, because of food, thou walkest not in love. On account of food, destroy not him for whom Messiah died.
16 Kada ka bar abin da ka ɗauka a matsayi kyakkyawa yă zama abin zargi ga waɗansu.
And let not our good thing be matter of reproach.
17 Gama mulkin Allah ba batun ci da sha ba ne, sai dai na adalci, salama, da kuma farin ciki cikin Ruhu Mai Tsarki,
For the kingdom of God, is not food and drink; but is righteousness, and peace, and joy in the Holy Spirit.
18 duk kuwa wanda yake bauta wa Kiristi a haka yana faranta wa Allah rai ne, yardajje kuma ga mutane.
For he who is in these things a servant of Messiah, is pleasing to God, and approved before men.
19 Saboda haka sai mu yi iya ƙoƙari mu aikata abin da zai kawo salama da kuma ingantawa ga juna.
Now let us strive after peace, and after the edification of one another.
20 Kada ku lalatar da aikin Allah saboda abinci. Dukan abinci mai tsabta ne, sai dai ba daidai ba ne mutum yă ci abin da zai sa wani yă yi tuntuɓe.
And let us not, on account of food, destroy the work of God. For every thing is, indeed, pure; yet it is evil, to the man who eateth with stumbling.
21 Ya fi kyau kada ka ci nama ko ka sha ruwan inabi ko kuma ka yi wani abin da zai sa ɗan’uwanka yă fāɗi.
It is proper, that we neither eat flesh, nor drink wine, nor do any thing, whereby our brother is stumbled.
22 Bari duk ra’ayin da kake da shi game da wannan sha’ani yă kasance tsakaninka da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa ba tă ba shi laifi game da abin da shi da kansa ya ɗauka cewa daidai ne ba.
Thou art one in whom there is faith; keep it to thyself, before God. Blessed is he, who doth not condemn himself, in that thing which he alloweth.
23 Amma wanda yake da shakka yakan jawo wa kansa hukunci ne in ya ci, domin yana ci ne ba bisa ga bangaskiya ba; kuma duk abin da bai zo daga bangaskiya ba zunubi ne.
For he who eateth and doubteth, is condemned; because he eateth not in faith. For every thing which is not of faith, is sin.