< Romawa 14 >

1 Ku karɓi wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, amma fa kada ku hukunta shi a kan abubuwan da ake da shakka a kai ba.
Him that is weak in his faith, receive ye, —not for disputing opinions: —
2 Bangaskiyar mutum ta yarda masa yă ci kome, amma wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, yakan ci kayan lambu ne kawai.
One, indeed, hath faith to eat all things, whereas, he that is weak, eateth herbs:
3 Mutumin da yake cin kowane irin abinci, kada yă rena wanda ba ya cin, wanda kuma ba ya cin kowane irin abinci, kada yă ga laifin mutumin da yake ci, domin Allah ya riga ya karɓe shi.
Let not, him that eateth, despise him that eateth not, and let not, him that eateth not, judge him that eateth; for, God, hath received him.
4 Kai wane ne har da za ka ga laifin bawan wani? Ko bawan yă yi aiki mai kyau, ko yă kāsa, ai, wannan ruwan maigidansa ne. Za a ma tsai da shi, domin Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
Who art, thou, that judgest another’s domestic? To his own master, he standeth or falleth; he shall, however, be made to stand, —for his master is able to make him stand.
5 Wani yakan ɗauki wata rana da daraja fiye da sauran ranaku; wani kuma yana ganin dukan ranakun ɗaya ne. Ya kamata kowa yă kasance da tabbaci a cikin zuciyarsa.
[For], one, indeed esteemeth one day beyond another, whereas, another, esteemeth every day: —let, each one, in his own mind be fully persuaded.
6 Wannan mai ɗaukan rana ɗaya da muhimmanci fiye da sauran, yana yin haka ne ga Ubangiji. Wannan mai cin nama, yana yin haka ne ga Ubangiji, gama yakan yi godiya ga Allah; wannan da ba ya ci kuwa, yana yin haka ne ga Ubangiji yana kuwa yin godiya ga Allah.
He that regardeth the day, unto the Lord, regardeth it, —and, he that eateth, unto the Lord, doth eat, for he giveth thanks unto God; and, he that eateth not, unto the Lord, doth not eat and give God thanks.
7 Gama ba waninmu da yake rayuwa wa kansa kaɗai, kuma ba waninmu da kan mutu don kansa kaɗai.
For, none of us, unto himself liveth, and, none, unto himself dieth;
8 In muna rayuwa, muna rayuwa ne ga Ubangiji; in kuma muna mutuwa, muna mutuwa ne ga Ubangiji. Saboda haka, ko muna a raye ko muna a mace, mu na Ubangiji ne.
For both, if we live, unto the Lord, we live, and, if we die, unto the Lord, we die; whether therefore we live, the Lord’s, we are; or whether we die, the Lord’s, we are;
9 Saboda wannan ne Kiristi ya mutu, ya kuma sāke rayuwa domin yă zama Ubangiji na matattu da na masu rai.
For, to this end, Christ died and lived, in order that, both of dead and living, he might have lordship.
10 Kai kuwa, don me kake ganin laifin ɗan’uwanka? Ko kuma don me kake rena ɗan’uwanka? Gama duk za mu tsaya a gaban kujerar shari’ar Allah.
But, thou, why dost thou judge thy brother? Aye! and thou, why dost thou despise thy brother? For, all of us, shall present ourselves unto the judgment seat of God;
11 A rubuce yake cewa, “‘Muddin ina raye,’ in ji Ubangiji, ‘kowace gwiwa za tă durƙusa a gabana; kowane harshe kuma zai furta wa Allah.’”
For it is written—Living am, I, saith the Lord, unto me, shall bow every knee, and, every tongue, shall openly confess unto God.
12 Don haka kowannenmu zai ba da lissafin kansa ga Allah.
Hence, [then], each one of us, of himself shall give account unto God.
13 Saboda haka bari mu daina ba wa juna laifi. A maimakon, sai kowa yă yi niyya ba zai sa dutsen tuntuɓe ko abin sa fāɗuwa a hanyar ɗan’uwansa ba.
No longer, then, upon one another, let us be sitting in judgment, but, this, judge ye rather—not to be putting a cause of stumbling before your brother or an occasion to fall.
14 A matsayina na mai bin Ubangiji Yesu na tabbata ƙwarai cewa babu abincin da yake marar tsabta don kansa. Amma in wani ya ɗauka wani abu marar tsabta ne, to, a gare shi marar tsabta ne.
I know and am persuaded in the Lord Jesus—that, nothing, is profane of itself, —save to him who reckoneth anything to be profane, unto that man, [it is] profane,
15 In kana ɓata wa ɗan’uwanka zuciya saboda abincin da kake ci, ba halin ƙauna kake nunawa ba ke nan. Kada abincin da kake ci yă zama hanyar lalatar da ɗan’uwanka wanda Kiristi ya mutu dominsa.
If, in fact, because of food, thy brother is being grieved, no longer, by the rule of love, art thou walking: —do not, by thy food, that man, be destroying, on whose behalf Christ died!
16 Kada ka bar abin da ka ɗauka a matsayi kyakkyawa yă zama abin zargi ga waɗansu.
Therefore, suffer not to be defamed, your own good thing;
17 Gama mulkin Allah ba batun ci da sha ba ne, sai dai na adalci, salama, da kuma farin ciki cikin Ruhu Mai Tsarki,
For the kingdom of God is not eating and drinking, but righteousness and peace and joy in Holy Spirit;
18 duk kuwa wanda yake bauta wa Kiristi a haka yana faranta wa Allah rai ne, yardajje kuma ga mutane.
For, he that in this doeth service unto the Christ, is acceptable unto God, and approved unto men.
19 Saboda haka sai mu yi iya ƙoƙari mu aikata abin da zai kawo salama da kuma ingantawa ga juna.
Hence, then, the things pertaining to peace, let us pursue, and the things which belong to the upbuilding one of another:
20 Kada ku lalatar da aikin Allah saboda abinci. Dukan abinci mai tsabta ne, sai dai ba daidai ba ne mutum yă ci abin da zai sa wani yă yi tuntuɓe.
Do not, for the sake of food, be throwing down the work of God! All things, indeed, are pure; but, ill, is it for the man who with occasion of stumbling doth eat, —
21 Ya fi kyau kada ka ci nama ko ka sha ruwan inabi ko kuma ka yi wani abin da zai sa ɗan’uwanka yă fāɗi.
Well, is it not to eat flesh nor to drink wine nor [to do aught] whereby thy brother is caused to stumble.
22 Bari duk ra’ayin da kake da shi game da wannan sha’ani yă kasance tsakaninka da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa ba tă ba shi laifi game da abin da shi da kansa ya ɗauka cewa daidai ne ba.
The faith which thou hast, have to thyself before God: happy, he that bringeth not judgment upon himself by that which he approveth;
23 Amma wanda yake da shakka yakan jawo wa kansa hukunci ne in ya ci, domin yana ci ne ba bisa ga bangaskiya ba; kuma duk abin da bai zo daga bangaskiya ba zunubi ne.
But, he that is in doubt, if he eat, hath condemned himself, —because, [it was] not of faith, and, everything which is not of faith, is sin.

< Romawa 14 >