< Romawa 14 >
1 Ku karɓi wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, amma fa kada ku hukunta shi a kan abubuwan da ake da shakka a kai ba.
ⲁ̅ⲡⲉⲧϭⲟⲟⲃ ⲇⲉ ϣⲟⲡϥ ⲉⲣⲱⲧⲛ ϩⲛ ⲧⲡⲓⲥⲧⲓⲥ ⲉϩⲉⲛϩⲟⲧϩⲧ ⲁⲛ ⲙⲙⲟⲕⲙⲉⲕ
2 Bangaskiyar mutum ta yarda masa yă ci kome, amma wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, yakan ci kayan lambu ne kawai.
ⲃ̅ⲟⲩⲛ ⲡⲉⲧⲡⲓⲥⲧⲉⲩⲉ ⲙⲉⲛ ⲉⲟⲩⲉⲙ ⲛⲕⲁ ⲛⲓⲙ ⲡⲉⲧϭⲟⲟⲃ ⲇⲉ ϥⲟⲩⲙ ⲟⲩⲟⲟⲧⲉ
3 Mutumin da yake cin kowane irin abinci, kada yă rena wanda ba ya cin, wanda kuma ba ya cin kowane irin abinci, kada yă ga laifin mutumin da yake ci, domin Allah ya riga ya karɓe shi.
ⲅ̅ⲙⲡⲣⲧⲣⲉ ⲡⲉⲧⲟⲩⲱⲙ ⲥⲉϣϥ ⲡⲉⲧⲉⲛϥⲟⲩⲱⲙ ⲁⲛ ⲁⲩⲱ ⲙⲡⲣⲧⲣⲉ ⲡⲉⲧⲉⲛϥⲟⲩⲱⲙ ⲁⲛ ⲕⲣⲓⲛⲉ ⲙⲡⲉⲧⲟⲩⲱⲙ ⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲅⲁⲣ ⲡⲉⲛⲧⲁϥϣⲟⲡϥ ⲉⲣⲟϥ
4 Kai wane ne har da za ka ga laifin bawan wani? Ko bawan yă yi aiki mai kyau, ko yă kāsa, ai, wannan ruwan maigidansa ne. Za a ma tsai da shi, domin Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
ⲇ̅ⲛⲧⲕ ⲛⲓⲙ ⲉⲕⲕⲣⲓⲛⲉ ⲛⲟⲩϩⲙϩⲁⲗ ⲉⲙⲡⲱⲕ ⲁⲛ ⲡⲉ ⲉϥⲁϩⲉⲣⲁⲧϥ ⲉⲡⲉϥϫⲟⲉⲓⲥ ⲏ ⲉϥⲛⲁϩⲉ ϥⲛⲁⲁϩⲉ ⲇⲉ ⲉⲣⲁⲧϥ ⲟⲩⲛϭⲟⲙ ⲅⲁⲣ ⲙⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲉⲧⲁϩⲟϥ ⲉⲣⲁⲧϥ
5 Wani yakan ɗauki wata rana da daraja fiye da sauran ranaku; wani kuma yana ganin dukan ranakun ɗaya ne. Ya kamata kowa yă kasance da tabbaci a cikin zuciyarsa.
ⲉ̅ⲟⲩⲛ ⲡⲉⲧⲕⲕⲣⲓⲛⲉ ⲙⲉⲛ ⲛⲟⲩϩⲟⲟⲩ ⲡⲁⲣⲁ ⲟⲩϩⲟⲟⲩ ⲟⲩⲛ ⲡⲉⲧⲕⲕⲣⲓⲛⲉ ⲇⲉ ⲛϩⲟⲟⲩ ⲛⲓⲙ ⲡⲟⲩⲁ ⲡⲟⲩⲁ ⲙⲁⲣⲉϥⲧⲱⲧ ϩⲙ ⲡⲉϥϩⲏⲧ
6 Wannan mai ɗaukan rana ɗaya da muhimmanci fiye da sauran, yana yin haka ne ga Ubangiji. Wannan mai cin nama, yana yin haka ne ga Ubangiji, gama yakan yi godiya ga Allah; wannan da ba ya ci kuwa, yana yin haka ne ga Ubangiji yana kuwa yin godiya ga Allah.
ⲋ̅ⲡⲉⲧⲙⲉⲉⲩⲉ ⲉⲡⲉϩⲟⲟⲩ ⲉϥⲙⲉⲉⲩⲉ ⲉⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲁⲩⲱ ⲡⲉⲧⲟⲩⲱⲙ ⲉϥⲟⲩⲱⲙ ⲙⲡϫⲟⲉⲓⲥ ϥϣⲡϩⲙⲟⲧ ⲅⲁⲣ ⲛⲧⲉ ⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲁⲩⲱ ⲡⲉⲧⲉⲛϥⲟⲩⲱⲙ ⲁⲛ ⲉⲧⲉⲛϥⲟⲩⲱⲙ ⲁⲛ ⲙⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲁⲩⲱ ϥϣⲡϩⲙⲟⲧ ⲛⲧⲙ ⲡⲛⲟⲩⲧⲉ
7 Gama ba waninmu da yake rayuwa wa kansa kaɗai, kuma ba waninmu da kan mutu don kansa kaɗai.
ⲍ̅ⲙⲛ ⲗⲁⲁⲩ ⲅⲁⲣ ⲙⲙⲟⲛ ⲟⲛϩ ⲛⲁϥ ⲁⲩⲱ ⲙⲛ ⲗⲁⲁⲩ ⲙⲙⲟⲛ ⲛⲁⲙⲟⲩ ⲛⲁϥ
8 In muna rayuwa, muna rayuwa ne ga Ubangiji; in kuma muna mutuwa, muna mutuwa ne ga Ubangiji. Saboda haka, ko muna a raye ko muna a mace, mu na Ubangiji ne.
ⲏ̅ⲉϣⲱⲡⲉ ⲅⲁⲣ ⲉⲛϣⲁⲛⲱⲛϩ ⲉⲛⲁⲱⲛϩ ⲙⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲁⲩⲱ ⲉϣⲱⲡⲉ ⲉⲛϣⲁⲛⲙⲟⲩ ⲉⲛⲁⲙⲟⲩ ⲙⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲉϣⲱⲡⲉ ϭⲉ ⲉⲛϣⲁⲛⲱⲛϩ ⲉϣⲱⲡⲉ ⲉⲛϣⲁⲛⲙⲟⲩ ⲁⲛⲟⲛ ⲛⲁ ⲡϫⲟⲉⲓⲥ
9 Saboda wannan ne Kiristi ya mutu, ya kuma sāke rayuwa domin yă zama Ubangiji na matattu da na masu rai.
ⲑ̅ⲉⲧⲃⲉ ⲡⲁⲓ ⲅⲁⲣ ⲁⲡⲉⲭⲥ ⲙⲟⲩ ⲁⲩⲱ ⲁϥⲱⲛϩ ϫⲉ ⲉϥⲉⲣϫⲟⲉⲓⲥ ⲉⲛⲉⲧⲙⲟⲟⲩⲧ ⲙⲛ ⲛⲉⲧⲟⲛϩ
10 Kai kuwa, don me kake ganin laifin ɗan’uwanka? Ko kuma don me kake rena ɗan’uwanka? Gama duk za mu tsaya a gaban kujerar shari’ar Allah.
ⲓ̅ⲛⲧⲟⲕ ⲇⲉ ⲁϩⲣⲟⲕ ⲕⲕⲣⲓⲛⲉ ⲙⲡⲉⲕⲥⲟⲛ ⲏ ⲁϩⲣⲟⲕ ϩⲱⲱⲕ ⲕⲥⲱϣϥ ⲙⲡⲉⲕⲥⲟⲛ ⲧⲛⲁⲁϩⲉⲣⲁⲧⲛ ⲅⲁⲣ ⲧⲏⲣⲛ ⲉⲡⲃⲏⲙⲁ ⲙⲡⲛⲟⲩⲧⲉ
11 A rubuce yake cewa, “‘Muddin ina raye,’ in ji Ubangiji, ‘kowace gwiwa za tă durƙusa a gabana; kowane harshe kuma zai furta wa Allah.’”
ⲓ̅ⲁ̅ϥⲥⲏϩ ⲅⲁⲣ ϫⲉ ϯⲟⲛϩ ⲁⲛⲟⲕ ⲡⲉϫⲉ ⲡϫⲟⲉⲓⲥ ϫⲉ ⲡⲁⲧ ⲛⲓⲙ ⲛⲁⲕⲱⲗϫ ⲛⲁⲓ ⲁⲩⲱ ⲗⲁⲥ ⲛⲓⲙ ⲛⲁⲉⲝⲟⲙⲟⲗⲟⲅⲉⲓ ⲙⲡⲛⲟⲩⲧⲉ
12 Don haka kowannenmu zai ba da lissafin kansa ga Allah.
ⲓ̅ⲃ̅ⲉⲓⲉ ⲉⲣⲉⲡⲟⲩⲁ ⲡⲟⲩⲁ ⲙⲙⲟⲛ ⲛⲁϯ ⲗⲟⲅⲟⲥ ϩⲁⲣⲟϥ ⲙⲡⲛⲟⲩⲧⲉ
13 Saboda haka bari mu daina ba wa juna laifi. A maimakon, sai kowa yă yi niyya ba zai sa dutsen tuntuɓe ko abin sa fāɗuwa a hanyar ɗan’uwansa ba.
ⲓ̅ⲅ̅ⲙⲡⲣⲧⲣⲉⲛⲕⲣⲓⲛⲉ ϭⲉ ϫⲓⲛ ⲧⲉⲛⲟⲩ ⲛⲛⲉⲛⲉⲣⲏⲩ ⲁⲗⲗⲁ ⲕⲣⲓⲛⲉ ⲛⲧⲟϥ ⲙⲡⲁⲓ ⲛϩⲟⲩⲟ ⲉⲧⲙⲕⲁϫⲣⲟⲡ ⲙⲡⲉⲕⲥⲟⲛ ⲏ ⲥⲕⲁⲛⲇⲁⲗⲟⲛ
14 A matsayina na mai bin Ubangiji Yesu na tabbata ƙwarai cewa babu abincin da yake marar tsabta don kansa. Amma in wani ya ɗauka wani abu marar tsabta ne, to, a gare shi marar tsabta ne.
ⲓ̅ⲇ̅ϯⲥⲟⲟⲩⲛ ⲁⲩⲱ ϯⲡⲓⲑⲉ ϩⲙ ⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲓⲏⲥ ϫⲉ ⲙⲛ ⲗⲁⲁⲩ ⲥⲟⲟϥ ϩⲁⲣⲟϥ ⲙⲁⲩⲁⲁϥ ⲉⲓⲙⲏⲧⲓ ⲙⲡⲉⲧⲙⲉⲉⲩⲉ ϫⲉ ⲡⲁⲓ ⲥⲟⲟϥ ⲉϥⲥⲟⲟϥ ⲙⲡ ⲉⲧⲙⲙⲁⲩ
15 In kana ɓata wa ɗan’uwanka zuciya saboda abincin da kake ci, ba halin ƙauna kake nunawa ba ke nan. Kada abincin da kake ci yă zama hanyar lalatar da ɗan’uwanka wanda Kiristi ya mutu dominsa.
ⲓ̅ⲉ̅ⲉϣϫⲉ ⲉⲧⲃⲉ ⲟⲩϩⲣⲉ ⲅⲁⲣ ⲡⲉⲕⲥⲟⲛ ⲗⲩⲡⲉⲓ ⲉⲓⲉ ⲁⲕⲗⲟ ⲉⲕⲙⲟⲟϣⲉ ⲕⲁⲧⲁ ⲟⲩⲁⲅⲁⲡⲏ ϩⲣⲁⲓ ϩⲛ ⲧⲉⲕϩⲣⲉ ⲙⲡⲣⲙⲉⲩⲧⲡⲏ ⲉⲛⲧⲁ ⲡⲉⲭⲥ ⲙⲟⲩ ϩⲁⲣⲟϥ
16 Kada ka bar abin da ka ɗauka a matsayi kyakkyawa yă zama abin zargi ga waɗansu.
ⲓ̅ⲋ̅ⲙⲡⲣⲧⲣⲉⲩϫⲓⲟⲩⲁ ϭⲉ ⲉⲡⲉⲛⲁⲅⲁⲑⲟⲛ
17 Gama mulkin Allah ba batun ci da sha ba ne, sai dai na adalci, salama, da kuma farin ciki cikin Ruhu Mai Tsarki,
ⲓ̅ⲍ̅ⲛⲧⲙⲛⲧⲣⲣⲟ ⲅⲁⲣ ⲁⲛ ⲙⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲡⲉ ⲟⲩⲱⲙ ϩⲓⲥⲱ ⲁⲗⲗⲁ ⲟⲩⲇⲓⲕⲁⲓⲟⲥⲩⲛⲏ ⲧⲉ ⲙⲛ ⲟⲩⲉⲓⲣⲏⲛⲏ ⲙⲛ ⲟⲩⲣⲁϣⲉ ϩⲙ ⲡⲉⲡⲛⲁ ⲉⲧⲟⲩⲁⲁⲃ
18 duk kuwa wanda yake bauta wa Kiristi a haka yana faranta wa Allah rai ne, yardajje kuma ga mutane.
ⲓ̅ⲏ̅ⲡⲉⲧϩⲙ ⲡⲁⲓ ⲅⲁⲣ ⲉⲧⲟ ⲙϩⲙϩⲁⲗ ⲙⲡⲉⲭⲥ ϥⲣⲁⲛⲁϥ ⲙⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲁⲩⲱ ⲟⲩⲥⲱⲧⲡ ⲛⲣⲱⲙⲉ ⲡⲉ
19 Saboda haka sai mu yi iya ƙoƙari mu aikata abin da zai kawo salama da kuma ingantawa ga juna.
ⲓ̅ⲑ̅ⲁⲣⲁ ϭⲉ ⲙⲁⲣⲛⲡⲱⲧ ⲛⲥⲁ ⲛⲁ ϯⲣⲏⲛⲏ ⲁⲩⲱ ⲛⲁ ⲡⲕⲱⲧ ⲉϩⲟⲩⲛ ⲉⲛⲉⲛⲉⲣⲏⲩ
20 Kada ku lalatar da aikin Allah saboda abinci. Dukan abinci mai tsabta ne, sai dai ba daidai ba ne mutum yă ci abin da zai sa wani yă yi tuntuɓe.
ⲕ̅ⲉⲧⲃⲉ ⲟⲩϩⲣⲉ ⲙⲡⲣⲕⲁⲧⲁⲗⲩ ⲙⲡϩⲱⲃ ⲙⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲥⲉⲟⲩⲁⲁⲃ ⲙⲉⲛ ⲧⲏⲣⲟⲩ ⲁⲗⲗⲁ ϥϩⲟⲟⲩ ⲙⲡⲣⲱⲙⲉ ⲉⲧⲛⲁⲟⲩⲱⲙ ϩⲓⲧⲛ ⲟⲩϫⲣⲟⲡ
21 Ya fi kyau kada ka ci nama ko ka sha ruwan inabi ko kuma ka yi wani abin da zai sa ɗan’uwanka yă fāɗi.
ⲕ̅ⲁ̅ⲛⲁⲛⲟⲩ ⲧⲙⲟⲩⲉⲙ ⲁϥ ⲟⲩⲇⲉ ⲉⲧⲙⲥⲉ ⲏⲣⲡ ⲟⲩⲇⲉ ⲡⲉⲧⲉⲣⲉ ⲡⲉⲕⲥⲟⲛ ⲛⲁϫⲓϫⲣⲟⲡ ⲛϩⲏⲧϥ ⲏ ⲛϥⲥⲕⲁⲛⲇⲁⲗⲓⲍⲉ ⲏ ⲛϥϭⲃⲃⲉ
22 Bari duk ra’ayin da kake da shi game da wannan sha’ani yă kasance tsakaninka da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa ba tă ba shi laifi game da abin da shi da kansa ya ɗauka cewa daidai ne ba.
ⲕ̅ⲃ̅ⲛⲧⲟⲕ ⲟⲩⲛⲧⲕ ⲟⲩⲡⲓⲥⲧⲓⲥ ⲕⲁⲁⲥ ⲛⲁⲕ ⲙⲡⲉⲙⲧⲟ ⲉⲃⲟⲗ ⲙⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲛⲁⲓⲁⲧϥ ⲙⲡⲉⲧⲉⲛϥⲛⲁⲕⲣⲓⲛⲉ ⲙⲙⲟϥ ⲁⲛ ϩⲙ ⲡⲉⲧϥⲇⲟⲕⲓⲙⲁⲍⲉ ⲙⲙⲟϥ
23 Amma wanda yake da shakka yakan jawo wa kansa hukunci ne in ya ci, domin yana ci ne ba bisa ga bangaskiya ba; kuma duk abin da bai zo daga bangaskiya ba zunubi ne.
ⲕ̅ⲅ̅ⲡⲉⲧⲛⲁⲣϩⲏⲧ ⲇⲉ ⲥⲛⲁⲩ ⲉϥϣⲁⲛⲟⲩⲱⲙ ϥⲧϭⲁⲉⲓⲏⲩ ϫⲉ ⲛⲧⲁϥⲁⲁⲥ ⲁⲛ ϩⲛ ⲟⲩⲡⲓⲥⲧⲓⲥ ϩⲱⲃ ⲇⲉ ⲛⲓⲙ ⲉⲧⲉ ⲛϩⲉⲛⲉⲃⲟⲗ ⲁⲛ ⲛⲉ ϩⲛ ⲟⲩⲡⲓⲥⲧⲓⲥ ϩⲉⲛⲛⲟⲃⲉ ⲛⲉ