< Romawa 13 >

1 Dole kowa yă yi biyayya ga masu mulki, gama babu wani iko sai ko in Allah ya yarda. Duk hukumomin da muke su, naɗin Allah ne.
E A HOOLOHE na kanaka a pau i ka ke alii maluna iho; no ka mea, aole alii, ke ae ole mai ke Akua; a o ka poe e alii ana, na ke Akua no lakou i hooalii mai.
2 Saboda haka, duk wanda ya yi tawaye ga hukuma yana yin tawaye da abin da Allah ya naɗa ne, waɗanda kuwa suke aikata haka, za su jawo wa kansu hukunci.
No ia mea, o ka mea e hoole i ka ke alii, oia ke hoole i ka ke Akua kauoha: a o ka poe hoole, o lakou ke hoahewaia.
3 Gama masu mulki ba abin tsoro ba ne ga waɗanda suke yin abin da yake daidai, sai dai ga waɗanda suke aikata laifi. Kana so ka rabu da jin tsoron wanda yake mulki? To, sai ka aikata abin da yake daidai, zai kuwa yabe ka.
No ka mea, aohe mea makau na alii no na hana maikai, aka, no na hana ino. Aole anei oe e makau i ko alii? E hana oe i ka mea pono, a e hoaponoia mai no oe e ia.
4 Gama shi bawan Allah ne don kyautata rayuwarka. Amma in ka aikata mugunta, to, sai ka ji tsoro, don ba a banza ne shugaba yake ɗaukan takobinsa ba. Shi fa bawan Allah ne, ta wurinsa ne fushin Allah yakan hukunta masu laifi.
No ka mea, he kauwa ia na ke Akua e pono ai oe. Aka, ina e hana oe i ka hewa, e makau no oe; no ka mea, aole he mea ole kona lawe ana i ka pahikaua; no ka mea, o ke kauwa ia na ke Akua, he ilamuku e hoopai ana i ka mea hana hewa.
5 Saboda haka, dole a yi biyayya ga hukumomi, ba don gudun horo kawai ba amma don lamirinku.
No ia mea, he mea pono no kakou e hoolohe aku, aole no ka inaina wale no, aka, no ka manao aku i ka pono kekahi.
6 Shi ne ma ya sa kuke biyan haraji, gama hukumomin nan bayin Allah ne, waɗanda suke ba da dukan lokacinsu don aikin shugabanci.
Nolaila hoi, ho pono no oukou e hookupu aku kekahi; no ka mea, he poe lawehana lakou na ke Akua e malama ana ia mea.
7 Ku ba wa kowa hakkinsa. In kuna da bashin haraji, sai ku biya; in kuɗin shiga ne, ku biya kuɗin shiga; in ladabi ne, ku yi ladabi; in kuma girmamawa ne, ku ba da girma.
Nolaila, e haawi aku i na kanaka a pau i ka lakou; i ka waiwai auhau i ka mea ho pono nona ke auhau mai; a i ke dute i ka mea he pono nona ke ohi mai; a i ka makau i ka mea he pono ke makauia ku; a i ka hoomaikai i ka mea he pono ko hoomaikaiia'ku.
8 Kada hakkin kowa yă zauna a kanku, sai dai na ƙaunar juna, don mai ƙaunar maƙwabcinsa ya cika Doka ke nan.
Mai noho a aie wale i ka kekahi, anoai ma ke aloha i kekahi i kekahi; no ka mea, o ka mea i aloha ia hai, oia ke malama i ko kanawai.
9 Umarnan nan, “Kada ka yi zina.” “Kada ka yi kisankai.” “Kada ka yi sata.” “Kada kuma ka yi ƙyashi.” Da dai duk sauran umarnai an ƙunshe su ne a wannan kalma “Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.”
No ka mea, eia, Mai moe kolohe oe; Mai pepehi kanaka oe; Mai aihue oe; Mai hoike wahahee oe; Mai kuko wale oe: a ina he kana wai e ae, ua komo poko ia iloko o keia olelo, o nei, E aloha oe i kou hoalauna e like me oe iho.
10 Ƙauna ba ta cutar da maƙwabci. Saboda haka ƙauna cika Doka ce.
Aole e hana hewa ana ke aloha i kona hoalauna; nolaila o ke aloha ka hooko ana i ke kanawai.
11 Ku yi wannan domin kun san irin zamanin da kuke ciki. Lokaci ya yi da za ku farka daga barcinku, don cetonmu ya yi kusa yanzu fiye da lokacin da muka fara ba da gaskiya.
Oia hoi, e hoomanao ana oukou i ka manawa, eia ka hora e ala'i kakou mai ka hiamoe ana; no ka mea, ano ua kokoke ae ko kakou ola, i ko ka wa i manaoio ai kakou.
12 Dare fa ya kusan ƙarewa; gari kuma yana gab da wayewa. Saboda haka bari mu kawar da ayyukan duhu mu kuma yafa kayan yaƙi na haske.
Ua auwi ae nei ka po, ua kokoke mai hoi ke ao; nolaila e haalele aku kakou i na hana o ka pouli, a e aahu i na mea kaua no ka malamalama.
13 Bari mu tafiyar da al’amuranmu yadda ya dace a yi da rana, ba a cikin shashanci da buguwa ba, ba cikin fasikanci da rashin kunya ba, ba kuma cikin faɗa da kishi ba.
E hele pono kakou me ka hele ana i ka la; aole me ka uhauha ana a me ka ona ana, aole me ka moe kolohe ana a me ka makaleho ana, aole me ka hakaka ana a me ka ukiuki ana.
14 A maimakon haka, ku ɗauki halin Ubangiji Yesu Kiristi, kada kuma ku yi tunani game da yadda za ku gamsar da sha’awace-sha’awacen mutuntaka.
Aka, e aahu oukou i ka Haku ia Iesu Kristo, aole e hoomakaukau no ke kino mamuli o kona mau kuko.

< Romawa 13 >