< Romawa 11 >

1 To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
I say then, Hath God cast away his people? By no means. For I also am an Israelite, of the seed of Abraham, [of] the tribe of Benjamin.
2 Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce,
God hath not cast away his people which he foreknew. Know ye not what the scripture saith of Elijah? how he maketh intercession to God against Israel, saying,
3 “Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”?
Lord, they have killed thy prophets, and digged down thy altars; and I am left alone, and they seek my life.
4 Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”
But what saith the answer of God to him? I have reserved to myself seven thousand men, who have not bowed the knee to Baal.
5 Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri.
Even so then at this present time also there is a remnant according to the election of grace.
6 In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.
And if by grace, then [is it] no more of works: otherwise grace is no more grace. But if of works, then is it no more grace: otherwise work is no more work.
7 To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare,
What then? Israel hath not obtained that which he seeketh for; but the election hath obtained it, and the rest were blinded.
8 kamar yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya ba su ruhun ruɗewa, idanu don su kāsa gani, da kuma kunnuwa don su kāsa ji, har yă zuwa yau.”
(According as it is written, God hath given them the spirit of slumber, eyes that they should not see, and ears that they should not hear; ) to this day.
9 Dawuda kuma ya ce, “Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko, sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.
And David saith, Let their table be made a snare, and a trap, and a stumbling-block, and a recompense to them:
10 Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.”
Let their eyes be darkened, that they may not see, and bow down their back always.
11 Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi.
I say then, Have they stumbled that they should fall? By no means: but [rather] through their fall salvation [is come] to the Gentiles, to provoke them to jealousy.
12 Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!
Now if the fall of them [be] the riches of the world, and the diminishing of them the riches of the Gentiles; how much more their fullness?
13 Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa,
For I speak to you Gentiles, inasmuch as I am the apostle of the Gentiles, I magnify my office:
14 da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu.
If by any means I may incite to emulation [them who are] my flesh, and may save some of them.
15 Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba?
For if the rejection of them [be] the reconciling of the world, what [shall] the receiving [of them be], but life from the dead?
16 In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.
For if the first fruit [is] holy, the lump [is] also [holy]: and if the root [is] holy, so [are] the branches.
17 In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan,
And if some of the branches be broken off, and thou, being a wild olive-tree, art ingrafted among them, and with them partakest of the root and fatness of the olive-tree;
18 kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka.
Boast not against the branches. But if thou boastest, thou bearest not the root, but the root thee.
19 To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.”
Thou wilt say then, The branches were broken off, that I might be ingrafted.
20 Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro.
Well; because of unbelief they were broken off, and thou standest by faith. Be not high-minded, but fear:
21 Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.
For if God spared not the natural branches, [take heed] lest he also spare not thee.
22 Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka.
Behold therefore the goodness and severity of God: on them who fell, severity; but towards thee, goodness, if thou shalt continue in [his] goodness: otherwise thou also shalt be cut off.
23 In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su.
And they also, if they abide not still in unbelief, shall be ingrafted: for God is able to ingraft them again.
24 Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?
For if thou wast cut out of the olive-tree which is wild by nature, and wast ingrafted contrary to nature into a good olive-tree; how much more shall these, which are the natural [branches], be grafted into their own olive-tree?
25 Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
For I would not, brethren, that ye should be ignorant of this mystery, (lest ye should be wise in your own conceits) that blindness in part hath happened to Israel, until the fullness of the Gentiles shall be come in.
26 Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
And so all Israel shall be saved: as it is written, There shall come out of Sion the Deliverer, and shall turn away ungodliness from Jacob:
27 Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
For this [is] my covenant to them, when I shall take away their sins.
28 Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
As concerning the gospel, [they are] enemies for your sakes: but as concerning the election, [they are] beloved for the father's sakes.
29 gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
For the gifts and calling of God [are] without repentance.
30 Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu,
For as ye in times past have not believed God, yet have now obtained mercy through their unbelief;
31 haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku.
Even so have these also now not believed, that through your mercy they also may obtain mercy.
32 Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē g1653)
For God hath concluded them all in unbelief, that he might have mercy upon all. (eleēsē g1653)
33 Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace! Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike, hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!
O the depth of the riches both of the wisdom and knowledge of God! how unsearchable [are] his judgments, and his ways past finding out!
34 “Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa yă ba shi shawara?”
For who hath known the mind of the Lord? or who hath been his counselor?
35 “Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu, da Allah zai sāka masa?”
Or who hath first given to him, and it shall be recompensed to him again?
36 Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn g165)
For from him, and by him, and to him [are] all things: to whom [be] glory for ever. Amen. (aiōn g165)

< Romawa 11 >