< Romawa 11 >

1 To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
Then I say, Did God cast away his people? it could not be so. For I am indeed an Israelite, of the seed of Abraham, of the tribe of Benjamin.
2 Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce,
God did not cast away his people whom he foreknew. Do you not know what the scripture says in Elijah, how he makes intercession to God against Israel?
3 “Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”?
Lord, they have slain thy prophets, they have digged down thine altars: and I am left alone, and they are seeking my life.
4 Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”
But what says the answer to him? I have left unto myself seven thousand men, who have not bowed the knee to Baal.
5 Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri.
Thus then there is even at this time a remnant left according to the election of grace:
6 In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.
and if by grace, it is not at all by works: since in that case grace is no more grace.
7 To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare,
What then? Israel did not attain that which he was seeking, but the election obtained it, and the rest were hardened:
8 kamar yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya ba su ruhun ruɗewa, idanu don su kāsa gani, da kuma kunnuwa don su kāsa ji, har yă zuwa yau.”
as has been written, God has given them the spirit of slumber, eyes that they should not see, and ears that they should not hear, unto this day.
9 Dawuda kuma ya ce, “Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko, sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.
And David says, Let their table be made a snare, and a trap, and a stumblingblock, and a recompense unto them:
10 Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.”
and let their eyes be darkened, that they may not see, and bow down their back always.
11 Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi.
Then I say; Whether did they stumble that they may fall? it could not be so: but by their fall, salvation came to the Gentiles, in order to provoke them to jealousy.
12 Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!
But if the fall of them was the riches of the world, and the depletion of them the riches of the Gentiles; how much more their fulness?
13 Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa,
But I speak to you Gentiles. Inasmuch then as I am an apostle of the Gentiles, I glorify my ministry:
14 da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu.
if perchance I may provoke my flesh, and save some of them.
15 Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba?
For if the casting away of them was the reconciling of the world, what will their reception be, but life from the dead?
16 In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.
But if the first fruit was holy, the lump is also: if the root was holy, the branches are also.
17 In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan,
And if certain ones of the branches were broken off, and you being a wild olive-tree are grafted in among them, and have become a partaker of the root of the fatness of the olive-tree;
18 kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka.
boast not against the branches: but if you boast, you are not bearing the root, but the root you.
19 To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.”
Then you will say, The branches were broken off, that I may be grafted in.
20 Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro.
Beautifully; they were broken off by unbelief, but you stand by faith, Think not high things, but fear.
21 Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.
For if God spared not the natural branches, neither will he spare you.
22 Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka.
Then behold the goodness and severity of God: upon those who fell indeed, severity; but upon you the goodness of God, if you may abide in his goodness: since you too may be cut off.
23 In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su.
But these also, if they may not abide in unbelief, shall be grafted in: for God is able to graft them in again.
24 Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?
For if you, having been cut off the olive tree which is wild by nature, and contrary to nature were grafted into the good olive tree: how much more shall these, who are the natural branches, be grafted into their own olive tree?
25 Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
I do not wish you to be ignorant, brethren, as to this mystery, in order that you may not he wise with yourselves, that blindness in part has happened unto Israel, until the fulness of the Gentiles may come in;
26 Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
and so all Israel shall be saved: as has been written, A leader shall come out of Zion, shall turn ungodliness from Jacob.
27 Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
And this is the covenant with me unto them, that I may take away their sins.
28 Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
They are enemies indeed, as touching the gospel, for your sakes: but beloved with reference to election for the sake of the fathers:
29 gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
for the gifts and calling of God are without repentance.
30 Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu,
For as you at one time were disobedient to God, but now you have received mercy through their disobedience,
31 haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku.
even also these were now disobedient, in order that through the mercy shown to you they themselves may now also obtain mercy.
32 Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē g1653)
For God has shut up all in unbelief, in order that he may have mercy on all. (eleēsē g1653)
33 Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace! Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike, hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!
O the depth of the riches of the wisdom of the knowledge of God! His judgments are unsearchable, and his ways past tracing out.
34 “Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa yă ba shi shawara?”
For who has known the mind of the Lord? who became his counsellor?
35 “Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu, da Allah zai sāka masa?”
or who has given unto him, and it shall be recompensed unto him again?
36 Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn g165)
Because of Him, and through him, and unto him, are all things: to him be glory forever: amen. (aiōn g165)

< Romawa 11 >